Monday, March 30
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyo: Bahaushiya dake zaune a kasar Ingila amma Bazawara ce na neman Mijin Aure daga Najeriya

Kalli Bidiyo: Bahaushiya dake zaune a kasar Ingila amma Bazawara ce na neman Mijin Aure daga Najeriya

Duk Labarai
Wata Bahaushiya me shekaru 33 wadda bazawarace tana zaune a kasar Ingila, tace tana neman mijin aure har daga Najeriya. Ga wanda ke so zai iya yin magana a kasan wannan Bidiyon ko ya aikawa matar me jawabi da lambar wayars. https://twitter.com/Hadeezaasabo/status/1931632926082396506?t=l3O5Uf9nXitwYOW1f6nGYA&s=19 Da yawa dai sun bayyana suna da ra'ayi amma kana iya gwada sa'arka.
Matawalle ya yi wa Dauda Lawal tayin shiga APC

Matawalle ya yi wa Dauda Lawal tayin shiga APC

Duk Labarai
Karamin ministan tsaron Najeriya, Bello Matawalle ya yi wa gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal tayin shiga jam'iyyar APC mai mulki. Ministan ya yi tayin ne ranar Asabar a garin mahaifarsa ta Maradun, lokacin da ya karɓi bakuncin dubban magoya bayansa da suka kai masa gaisuwar barka da sallah. Matawalle wanda ya kasance tsohon gwamnan Zamfara, ya ce APC jam'iyya ce ta mutanen kirki da dattako, don haka ya shawarci Dauda Lawal ya shiga jam'iyyar. Ministan ya ce maimakon gwamnan ya bi ta ɓarauniya hanya, gara ya fito fili ya bi hanyar da ta dace wajen shiga APC. "Ba ni da matsala da gwamnan idan yana son shiga APC. Ya zo ya bi sahun masu yunkurin kawo ci gaba a ɓangaren tsaro da zaman lafiya da kuma ayyukan raya ƙasa," in ji Matawalle. Ya kuma ce shugaba Bola Tinubu jagora ne na...
Bazan iya zama jam’iyya daya da El-Rufai ba, saboda bashi da akida>>Inji Sanata Wadada yace ya bar jam’iyyar SDP

Bazan iya zama jam’iyya daya da El-Rufai ba, saboda bashi da akida>>Inji Sanata Wadada yace ya bar jam’iyyar SDP

Duk Labarai
Sanata Ahmed Aliyu Wadada daga Jihar Nasarawa ya bayyana cewa ya bar jam'iyyar SDP. Ya bayyana cewa dalilinsa na barin jam'iyyar shine ba zai iya ci gaba da zama da wadanda basu da akida a jam'iyya daya ba. Ya bayyana hakanne a hirarsa da 'yan jarida inda yace Musamman Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, yace bashi da akida. Yace El-Rufai na kan gaba wajan jawo hankalin mutane da cewa ya kamata mulki ya koma kudancin Najeriya. Ya kara da cewa shine ya ce a zabi Tinubu amma saboda bai samu mukamin Minista ba amma ya bar jam'iyyar.
Fasto ya caccaki Shugaba Tinubu daboda fara yakin neman zabe shekaru 2 kamin zabe

Fasto ya caccaki Shugaba Tinubu daboda fara yakin neman zabe shekaru 2 kamin zabe

Duk Labarai
Babban Fasto a jihar Kaduna, Reverend Timothy Yahaya ya caccaki shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu inda ya bayyana cewa, yayi wuri a fara yakin neman zaben. Yace yana kiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da ya dakatar da yakin neman zaben inda yace sai kwanaki 90 kamin zaben ya kamata a fara yakin neman zaben. Reverend Timothy Yahaya yace gaba daya an manta da yiwa mutane aiki inda aka koma yakin neman zabe wanda a baya ba haka tsarin yake ba a kasarnan.
Zulum ya bai wa iyalan sojojin da aka kàshè tallafin miliyan 100

Zulum ya bai wa iyalan sojojin da aka kàshè tallafin miliyan 100

Duk Labarai
Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai wa iyalan sojijin da aka kashe da kuma waɗanda aka jikkata a fagen daga a yaƙi da ƴan ta da ƙayar-baya a arewa maso gabas, tallafin naira miliyan 100. Gwamnan ya bayar da tallafin ne ranar Asabar yayin liyafar cin abinci a daidai lokacin da ake ci gaba da bukukuwan sallah, inda babban hafsan sojin ƙasa Laftanar-Janar Olufemi Oluyede da babban hafsan sojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar suka halarci liyafar a barikin sojoji na Maimalari a Maiduguri. Zulum ya gabatar da chekin kuɗin na naira miliyan 100 ga hannun kwamandan dakarun Haɗin-Kai, Manjo-janar Abdussalam Abubakar. Ya bayyana cewa kowane soja da aka raunata a fagen daga zai samu naira 500,000, yayin da za a raba sauran kuɗin ga iyalan sojojin da aka kashe. Gwamna Zulu...
Gwamnan Benue ya tona Asirin masu daukar nauyin hàrè-hàrèn ‘yan tà’àddà

Gwamnan Benue ya tona Asirin masu daukar nauyin hàrè-hàrèn ‘yan tà’àddà

Duk Labarai
Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, ya zargi wasu ƴan siyasa da ke ci a majalisar tarayya da ɗaukar nauyin hare-hare da ake kai wa jihar, inda ya ce ba za su lamunci hakan ba. Gwamnan ya yi wannan zargi ne yayin tattaunawa a shirin 'Politics Today' na gidan talabijin na Channels. Duk da cewa bai bayyana sunayen ƴan siyasar ba, gwamnan ya ce kwamitin da ya naɗa domin yin binciken kan batun kai hare-haren ya gano akwai sunayen manyan ƴan siyasa, inda ya sha alwashin ɗaukar mataki nan take idan ya karɓi rahoton kwamitin a mako mai zuwa. "Abin takaici yadda wasu manyan ƴan siyasa ke ci gaba da bai wa ƴan bindigar da ke kai hare-haren mafaka da kuma saya musu makamai. Za mu ɗauki mataki tun da ba su damu da irin rayuka da suke salwantar wa ba," in ji gwamna Alia. Jihar ta Benue...
Mun kaiwa masu ikirarin Jìhàdì mummunan hàrì>>Sojojin Najeriya

Mun kaiwa masu ikirarin Jìhàdì mummunan hàrì>>Sojojin Najeriya

Duk Labarai
Sojojin Najeriya sun bayyana cewa, Sun kaiwa Masu ikirarin Jìhàdì mummunan hari ta jirgin sama a kauyen Talala da kauyen Ajigin dake yankin Timbuktu a jihar Borno. Hukumar sojojin tace ta lalata kayan amfanin maharan da yawa. An kai harinne ranar Asabar, 7 ga watan Mayu da misalin karfe 5:30 p.m. Hukumar tace ta kai harinne bayan samun bayanai cewa mayakan masu ikirarin Jihadi na taruwa dan kaiwa sojoji hari. Hukumar tace harin ya tarwatsa maharan inda da yawa suka jikkata kuma shirinsu ya lalace. Hukumar ta yi gargadin cewa, wannan gargadi ne cewa ko a inane makiyansu suke zasu kai musu hari su tarwatsa su.
‘Yan Bìndìgà sun sake kai mummunan hàrì a jihar Arewa

‘Yan Bìndìgà sun sake kai mummunan hàrì a jihar Arewa

Duk Labarai
'Yan Bindiga akalla 10 sun kai mummunan hari wani kauye me suna Chito dake karamar hukumar Ukum ta jihar Benue ranar Asabar. Maharan sun kai harinne da misalin karfe 2:26 am inda suka shafe awanni 2 da mintuna 30 suna aikata masha'a. Ance sun daki mutane da dama sannan suka saci kayan sawa da abinci da sauransu. Daya daga cikin wadanda abin ya shafa, Dr. Isaac H. Mamkaa wanda malamine a kwalejin ilimi ta Katsina Ala ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace 'yan Bindigar sun ce zasu sake komawa su kai musu hari garin.