Wednesday, July 15
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Bèllò Tùrjì ya ƙaƙaba harajin Naira Miliyan 50 kan manoma a Zamfara da Neja

Bèllò Tùrjì ya ƙaƙaba harajin Naira Miliyan 50 kan manoma a Zamfara da Neja

Duk Labarai
Bello Turji ya ƙaƙaba harajin Naira Miliyan 50 kan manoma a Zamfara da Neja {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Mazauna wasu yankunan da dama a jihohin Zamfara da Neja sun sake shiga wani mawuyacin hali, bayan da sanannen jagoran ƴan bindiga, Bello Turji, ya bukaci a biya naira miliyan 50 kafin a basu damar fara aikin noma na bana. LEADERSHIP ta rawaito cewa wannan bukatar ta fito fili ne ta bakin wani mai nazarin tsaro mai suna Bakatsine, wanda ya wallafa bayani a shafinsa na X , inda ya bayyana cewa shugaban ƴan ...
Sanata Lado ya miƙa kyaututtukan gidaje ga waɗanda su ka yi na ɗaya da na biyu a musabaƙar Kur’ani a Kano

Sanata Lado ya miƙa kyaututtukan gidaje ga waɗanda su ka yi na ɗaya da na biyu a musabaƙar Kur’ani a Kano

Duk Labarai
Sanata Lado ya miƙa kyaututtukan gidaje ga waɗanda su ka yi na ɗaya da na biyu a musabaƙar Kur'ani a Kano Sanata Bashir Lado ya miƙa kyaututtukan gidaje ga waɗanda su ka yi na ɗaya da na biyu a musabaƙar Kur'ani da aka kammala kwanannan a jihar Kano. Kyaututtukan sun haɗa da gidaje biyu masu dakuna biyu da falo ga wadanda suka yi na biyu a gasar , da kuma gidaje masu dakuna uku ga wadanda suka yi na ɗaya a musabaƙar. Wadanda suka samu nasarar sun hada da:Maryam Abubakar Mu'az (wacce ta zo ta ɗaya a izifi 60 a mata, Ahmad Shu'aib (wanda ya yi ma daya a izifi 60 a maza), Zainab Hassan Shu'aib (ta biyu a izifi 60 a mata), da Ahmad Kabir Baturi (na biyu a izifi 60 a maza). Da ya ke jawabi jim kadan bayan mika mukullayen gidajen, Sen.Lado, wanda ya shirya gasar, ya ce an gudanar da ...
Kalli Bidiyon yanda Wike yake taka rawa a wajan kaddamar da babban dakin taro na kasa da kasa dake Abuja

Kalli Bidiyon yanda Wike yake taka rawa a wajan kaddamar da babban dakin taro na kasa da kasa dake Abuja

Duk Labarai
Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya taka rawa a wajan kaddamar da gyaran da akawa babban dakin taro na kasa da kasa. A yayin kaddamarwar ya taka rawa. Kuma an sakawa dakin taron sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. https://twitter.com/channelstv/status/1932465426044236257?t=qnSAyxARa3IcYTrLTu6Ffw&s=19 Lamarin ya dauki hankula inda wasu suka yaba, wasu kuwa kushewa suka yi.
Kalli Bidiyo: Fasto ya bayyana cewa, Kiristoci ya kamata su rika layya ba Musulmai ba

Kalli Bidiyo: Fasto ya bayyana cewa, Kiristoci ya kamata su rika layya ba Musulmai ba

Duk Labarai
Wannan wani fasto ne da ya dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan cewa, Kiristoci ne ya kamata su rika layya ba musulmai ba. A cikin bidiyon wa'azinsa a cocinsa, Faston ya bayyana tarihin layyar inda yace sune suka fi alaka da ita ba musulmai ba. https://twitter.com/AsakyGRN/status/1931978207919542634?t=dPTtS3iOFejah7DlOGZ87w&s=19 Wasu dai sun yadda dashi inda wasu suka ce basu yadda ba.
Kalli Bidiyo:Fasto Jeremiah Omoto Fufeyin ya samar da rigar bacci ga mata wadda yace idan mace ta saka ta ko likitoci sun ce mijinta ya daina haihuwa sai ya mata ciki

Kalli Bidiyo:Fasto Jeremiah Omoto Fufeyin ya samar da rigar bacci ga mata wadda yace idan mace ta saka ta ko likitoci sun ce mijinta ya daina haihuwa sai ya mata ciki

Duk Labarai
Fasto Jeremiah Omoto Fufeyin ya bayyana cewa, ya samar da wata riklgar bacci ga mata wadda ko likita yace maniyyin mijinki ya tsinke, to idan kika saka rigar sai kin dauki ciki. Faston ya bayyana rigarne a cocinsa inda aka ganta dauke da hotunansa. https://twitter.com/dammiedammie35/status/1932178002495807492?t=3BXzkL3hLAI2kAiCZoVvgQ&s=19 Lamarin ya zowa mutane da mamaki matuka.
Idan na ci amanar Tinubu na zama shedan kuma Allah sai ya azabtar dani>> Ministan Ayyuka David Umahi

Idan na ci amanar Tinubu na zama shedan kuma Allah sai ya azabtar dani>> Ministan Ayyuka David Umahi

Duk Labarai
Ministan ayyuka, David Umahi ya bayyana cewa saboda yaddar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya masa, idan ya ci amanarsa ya zama shedan. Umahi yace Tinubu ya bashi aikin sayo kayan wani aiki da za'a yi da kudin suka kai Naira Tiriliyan 1.6, yace amma abin mamaki Tinubun bai taba kiransa ya ji ko ya ake ciki ba. Umahi yace na kowane zai iya maka wannan abin ba dan haka shi ya fada har a gaban Tinubu cewa, daga Allah sai shi a wadanda yake girmamawa dan yafi iyalansa. Umahi ya bayyana hakane a Abakaliki yayin ganawa da manema labarai.
Kalli Bidiyon yanda wata ‘yar kasuwa ta fashe da kuka bayan da ta aikawa kawarta Naira Miliyan 6 ta sayo mata jakunkuna daga kasar China amma ta aiko mata kwali ba komai a ciki

Kalli Bidiyon yanda wata ‘yar kasuwa ta fashe da kuka bayan da ta aikawa kawarta Naira Miliyan 6 ta sayo mata jakunkuna daga kasar China amma ta aiko mata kwali ba komai a ciki

Duk Labarai
Wannan wata budurwace data aikawa kawarta da Miliyan 6 ta sayo mata da jakunkuna daga kasar China. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1932439373796024600?t=QekclgWoU8diB80kAAua1g&s=19 Saidai ta aiko mata da kwali babu komai a ciki, lamarin yasa ya fashe da kuka tana fadin gaba daya kudinta ne ta aika mata.
Bawai son Tinubu ne yasa ‘yan siyasa ke tururuwar shiga APC ba, Kudin da suka sata na al’umma ne suke neman a yafe musu>>Solomon Dalung

Bawai son Tinubu ne yasa ‘yan siyasa ke tururuwar shiga APC ba, Kudin da suka sata na al’umma ne suke neman a yafe musu>>Solomon Dalung

Duk Labarai
Tsohon Ministan Matasa da Cigaban Wasanni, Solomon Dalung, ya ce ‘yan siyasar da suka fice daga jam’iyyun adawa zuwa jam’iyyar APC mai mulki suna yi ne kawai domin neman a share laifukansu ne na almundahana. Dalung wanda ya bayyana hakan ne a Abuja inda ya nuna rashin gamsuwarsa da cewa ’yan siyasa suna tururuwa zuwa jam’iyyar APC ne saboda ta yi aiki mai kyau, ko dan farin jininta da yi wa talaka aikin da ya dace. Dalung ya ce masu sauya shekar suna la'akari da kalaman tsohon Gwamnan Jihar Edo, Adams Oshiomhole da ya ce komai girman zunubansu, za a gafarta musu da zarar sun koma APC, ko da yake Oshiomhole ya musanta wannan magana da aka danganta shi da ita.