Karanta Abu biyar da ba ku sani ba kan Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi
Tun bayan rasuwar Sheikh Idris Abdul'aziz Dutsen Tanshi ƴan Najeriya musamman Musulmai ke ta faman yi masa addu'o'on nema masa gafara da kuma yin tambayoyin sanin haƙiƙanin wane ne marigayin.
Hakan ne ya sa BBC ta ji ta bakin Injiniya Ayuba Abdullahi Muhammad wanda ɗalibinsa ne kuma makusancinsa.
Haihuwa
An haifi Malam Idris Abdu'aziz Dutsen Tanshi a garin Gwaram da ke ƙaramar hukumar Alƙaleri a jihar ta Bauchi a shekarar 1957.
Marigayin ya yi doguwar jinya kafin rasuwar tasa, inda ya yi yawon neman magani a ƙasashen da suka haɗa da Saudiyya da Indiya.
Sheikh Tanshi ya rasu ya bar mahaifiyarsa da mata guda uku da kuma ƴaƴa 32.
Ilimi
Sheikh Idris Abdul'aziz ya kasance mutum mai son neman ilimi musamman bincike. Ya ƙware a fannin Shari'ar Musulunci inda ya yi digirinsa n...








