Sunday, February 22
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kamfanin mai na NNPCL ya rage farashin litar man fetur zuwa Naira 860.

Kamfanin mai na NNPCL ya rage farashin litar man fetur zuwa Naira 860.

Duk Labarai
Kamfanin mai na kasa NNPCL, ya rage farashin litar mai daga naira 920, zuwa naira 860. An samu wannan cigaba a daidai lokacin da ake samun gasa tsakanin manyan yan kasuwar mai dangane da farashin fetur, wanda a makon daya gabata matatar mai ta Dangote ta sanar da rage farashin litar man daga naira 890 zuwa naira 825. Haka zalika hawa da saukar farashin danyen mai a kasuwannin duniya na taimakawa wajen samun hawa da saukar farashin.
Kungiyar dalibai ta kasa NANS zata yi zanga-zangar kalubalantar rufe Makarantun Boko a wasu jihohin arewa saboda Azumin Ramadan.

Kungiyar dalibai ta kasa NANS zata yi zanga-zangar kalubalantar rufe Makarantun Boko a wasu jihohin arewa saboda Azumin Ramadan.

Duk Labarai
Kungiyar dalibai ta kasa NANS zata yi zanga-zangar kalubalantar rufe Makarantun Boko a wasu jihohin arewa saboda Azumin Ramadan. Kungiyar tace zata yi zanga-zangar ce in har jihohin Kano, Bauchi da Kebbi da Katsina basu janye umarnin rufe Makarantun da suka yi ba. Itama kungiyar Kristocin Najeriya ta kalubalanci rufe Makarantun. Wadannan jihohi sun bayar da hutun ne don saukakawa al'umma musamman Malamai wahalhalun Azumin.
An yiwa wannan faston daurin rai da rai bayan samunsa da laifin yiwa yarinya me shekaru 13 fyàdè

An yiwa wannan faston daurin rai da rai bayan samunsa da laifin yiwa yarinya me shekaru 13 fyàdè

Duk Labarai
Kotu dake za zama a jihar Ekiti a ranar Litinin dinnan ta daure wani Fasto me sunan Adeleye Akingbaso da shekaru 47 bisa laifin yiwa yarinya me shekaru 13 fyade. Wanda ake zargi din abokin mahaifiyar yarinyar da yawa fyadene. da take bayar da labarin yanda lamarin ya faru tace Adeleye yakan kwana a gidansu, tace ranar da abin zai faru mahaifiyarta tana aikin dare ne. Tace tana kwance ya tashe ta yace wai ta yi fitsarin kwance tace abin ya bata mamaki, nan dai ya ciro wani mai ya shafa mata a gabanta. Tace daga nan bata san abinda ya faru ba da ta tashi ta ga an yi mata fyade tace ya gargade ta da cewa idan ta fada zai kasheta. Tace a rana ta biyu ya isketa a dakin dafa abinci shima mahaifiyarta bata nan inda yace mata yana son kammala abinda ya fara saidai anan ta ki yadda i...
Majalisar Dattijai ta yi watsi da zargin da Sanata Natasha Akpoti kewa kakakin majalisar Godswill Akpabio na Làlàtà

Majalisar Dattijai ta yi watsi da zargin da Sanata Natasha Akpoti kewa kakakin majalisar Godswill Akpabio na Làlàtà

Duk Labarai
Majalisar dattijai ta ce bata da masaniya game da zargin da sanata Natasha Akpoti kewa kakakin majalisar, Sanata Godswill Akpabio na neman yin lalata da ita. Me magana da yawun majalisar, Senator Adeyemi Adaramodu ne ya bayyana haka a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Arise TV inda yace Sanata Natasha Akpoti bata gabatar wada kwamitin ladabtarwa na majalisar zarge-zargen da takewa Sanata Godswill Akpabio ba. Yace dan haka ba ruwansu da maganar ba zasu dauki mataki akan abinda ke faruwa a kafafen sadarwa na yanar gizo ba ko kuma gidajen watsa labarai ba.
Gwamnatin tarayya zata baiwa kananan ‘yan kasuwa da suka yi zarra Kyautar Naira Miliyan 220, duba rabar da za’a fara rijista

Gwamnatin tarayya zata baiwa kananan ‘yan kasuwa da suka yi zarra Kyautar Naira Miliyan 220, duba rabar da za’a fara rijista

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta sanar da aniyarta ta baiwa kanana da matsakaitan 'yan kasuwa kyautar kidade da gidaje da motoci. Me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar kananan da matsakaitan masana'antu Temitola Adekunle-Johnson ne ya bayyana hakan ranar Litinin. Yace zasu bude shafin yin rijista nan da 7 ga watan Maris inda za'a kulle yin rijistar ranar 7 ga watan Afrilu. Yace zasu duba irin gudummawar da kasuwanci ya kawowa Najeriya kamin su zabeshi.
Sunayen Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Da Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ba Su Lasisi A Zaman Majalisar Zartaswa Ta Kasa, Yau Litinin

Sunayen Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Da Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ba Su Lasisi A Zaman Majalisar Zartaswa Ta Kasa, Yau Litinin

Duk Labarai
Sunayen Jami'o'i 11 Masu Zaman Kansu Da Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ba Su Lasisi A Zaman Majalisar Zartaswa Ta Kasa, Yau Litinin. New City University, Ayetoro Ogun State University of Fortune, igbotako, Ondo State Eranova University, Mabushi Minaret University, Ikirun, Osun Annex Abubakar Toyin University, Oke-Agba, Kwara State Southern Atlantic University Uyo, Akwa Ibom State Lens University, ilemona, Kwara State Monarch University, Iyesi-Ota, Ogun State Tonnie Iredia University of Communication, Benin City Isaac Balami University of Aeronautics and Management, Lagos Kevin Eze University, Mgbowo, Enugu State Daga Jamilu Dabawa
Da Duminsa: An yi gàrkùwà da dansandan Najeriya a Abuja

Da Duminsa: An yi gàrkùwà da dansandan Najeriya a Abuja

Duk Labarai
Rahotanni daga babban birnin tarayya Abuja na cewa wasu da ake zargin masu garkuwa da mutanene sun sace dansandan Najeriya da wasu mutane. Rahoton yace an sace CSP Modestus Ojiebe ne akan hanyar Abuja zuwa Kaduna. Dansandan dake aiki a Kwara an yi garkuwa dashine a lokacin da yake kokarin gyaran motarsa da ta lalace a kusa da barikin 'yansanda dake Dei-Dei. Rahoton yace wata motace ta je kusa dashi ta yi fakin inda mutane dauke da makamai su 4 suka fito daga cikinta suka kwace mai wayoyinsa dana matarsa, saidai da suka ga shaidar katin aikin dansanda, sun yi garkuwa dashi inda suka jefashi cikin mota suka tafi dashi. Tuni dai aka saka jami'an tsaro a hanyoyin shiga da fita birnin Abuja. Wasu 'yansanda sun tabbatar wa da Jaridar Daily Trust da wannan labari saidai har yanzu h...
Malamin Jami’ar Ahmadu Bello Dake Zaria Ya Rasu Yana Tsakar Sallar Tarawih

Malamin Jami’ar Ahmadu Bello Dake Zaria Ya Rasu Yana Tsakar Sallar Tarawih

Duk Labarai
INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Allah Ya Yi Wa Dakta Musa Bara'u Gamji, Na Sashen Koyan Aikin Jarida A Jami'ar Ahmadu Bello Dake Zaria, Rasuwa Yana Tsakar Sallar Tarawih, Jiya Lahadi A Birnin Gusau, Jihar Zamfara. An Yi Jana'izarsa Kamar Yadda Addinin Musulunci Ya Tanada A Masallacin Juma'a Na Imam Malik Dake Birnin Gusau, Jihar Zamfara Yau Litinin. Allah Ya Jikansa Da Rahama! Daga Jamilu Dabawa
Wasu bala’o’i sun aukawa kasar Amurka inda A birnin Los Angeles aka yi girgizar kasa, a South Carolina gobarar daji ce ta kunno kai

Wasu bala’o’i sun aukawa kasar Amurka inda A birnin Los Angeles aka yi girgizar kasa, a South Carolina gobarar daji ce ta kunno kai

Duk Labarai
An samu girgizar kasa me maki 3.9 a birnin Los Angeles na Jihar California ta kasar Amurka. Hakan na zuwane bayan da aka kammala bikin bayar da kyautar Oscar 2025. Gurare da yawa da suka hada da Pasadena, Long Beach, San Fernando Valley, Torrance, Redondo Beach da Glendale sun bayyana cewa sun ji motsin kasa. Babu dai rahoton cewa wani ya ji rauni. Hakan na zuwane kwanaki kadan bayan da aka samu mummunar gobarar daji a birnin na Los Angeles. Hakanan a jihohin South Carolina da North Carolina na kasar Amurkar ma Wutar daji ce ta barke inda ake maganar taci kadada sama da 1,600 a South Carolina inda a North Carolina kuma taci kadada sama da 500. Mahukunta a yankunan da gobarar ta tashi sun bayar da umarnin mutane su fice daga yankunan.