Saturday, February 21
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kungiyar Kwadago ta NLc na barazanar shiga yajin aiki saboda karin kudin kiran waya dana data

Kungiyar Kwadago ta NLc na barazanar shiga yajin aiki saboda karin kudin kiran waya dana data

Duk Labarai
Kungiyar Kwadago ta NLC ta yi barazanar shiga yajin aiki muddin gwamnati bata mutunta alkawarin da suma cimmawa ba. Kungiyar ta bayyana cewa sun cimma matsayar cewa za'a rage karin kudin kiran waya dana data da aka yi da kaso 50 zuwa 35. Kungiyar tace idan Gwamnatin ta kasa mutunta wannan yarjejeniyar sun sanar da wakilansu na fadin Najeriya cewa su shirya yin zanga-zanga.
Sanata Barau ya ce zai goyi bayan ƙirƙiro jihar Karaɗuwa

Sanata Barau ya ce zai goyi bayan ƙirƙiro jihar Karaɗuwa

Duk Labarai
Mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya, Sanata Barau Jibrin ya ce zai yi aiki tare da Sanata Muntari Dan-Dutse mai wakiltar yankin Funtua na jihar Katsina domin tabbatar da ƙirƙiro jihar Karaɗuwa daga jihar Katsina ta arewa maso yamma, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito a shafinta na intanet. Ya ce ƙirƙiro sabuwar jiha zai taimaka wajen ci gaba da haɓaka tattalin arzikin yankin da mutanenta. "Zan yi aiki tare da ɗan'uwana, Sanata Muntari Dan-Dutse domin ganin an ƙirƙiri jihar ta Karaɗuwa daga jihar Katsina. Yankin Karaɗuwa na da duk abin da ake buƙata domin zama jiha. Ina goyon bayan buƙatar nan ta mutanen yankin duk da cewa lamari ne mai wahala," in ji shi. Barau ya bayyana haka ne a lokacin da yake jagorantar rabon tallafin kayan abinci na azumi ga dubban ...
Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio – Mijin Natasha

Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio – Mijin Natasha

Duk Labarai
Mijin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, Emmanuel Oritsejolomi Uduaghan ya magantu game da rikicin da ke tsakanin matarsa da shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio. Mijin, wanda basarake ne a yankin Neja Delta ya ce matarsa ta faɗa masa lokacin da Akpabio ya ci zarafinta, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito. "Da kaina na je na same shi na buƙaci ya ba matata girman da ta cancanta, sannan ya girmama abotan da ke tsakaninmu. Bayan mun tattauna sai muka amince da a warware maganar cikin mutunci. "Amma bayan maganar da muka yi, sai matata ta cigaba da bayyana damuwa game da irin cin zarafin da take fuskanta daga shugaban majalisar dattawar. "Ni dai na yarda da matata, kuma aure muka yi na soyayya da ƙauna. Babu abin da ya fiye min ita a yanzu domin ita ce...
Ramadan: Coci ya raba wa musulmi kayan abinci a Kaduna

Ramadan: Coci ya raba wa musulmi kayan abinci a Kaduna

Duk Labarai
Cocin Christ Evangelical and Life Intercessory Ministry da ke unguwar Sabon Tasha a ƙaramar hukumar Chikun a jihar Kaduna ya raba wa musulmi masu ƙananan ƙarfi da makarantun addinin musulunci kayan abinci domin su samu abin sakawa a bakin salati a lokacin azumi. Shugaban coci, Fasto Yohanna Buru ne ya jagoranci raba kayan abincin, inda ya ce ya yi haka ne domin ƙarfafa zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin musulmi da kirista. "Muna mayar da biki ne kan yadda Hajiya Ramatu Tijjani take yawan ba kirista kayan abinci a lokacin bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara," in ji shi, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito. Fasto Buru ya ce suna da burin tallafa wa aƙalla mutum 1,000 ne a azumin na bana, sannan ya ce ya jagoranci haɗa malamai da fastoci aƙalla guda 30 domin...
In kana da kudi, zaka iya siye kowa a kasarnan ka ci zabe>>Inji Tsohon Gwamnan Imo

In kana da kudi, zaka iya siye kowa a kasarnan ka ci zabe>>Inji Tsohon Gwamnan Imo

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Imo, Achike Udenwa ya bayyana cewa lamarin siyasa da mulki a kasarnan ya tabarbare inda komai ya koma maganar kudi. Yace idan kana da kudi, zaka iya saye Sojoji, 'yansansa, Hukumar zabe dama masu zaben. Ya bayyana hakane a wajan wata hira da aka yi dashi. Yace yanzu idan mutum ya fito neman zabe babu maganar me zaiwa mutane ko menene halinsa, kudi kawai ake dubawa, kowa yana duba me zai samu.
Ina da addu’ar da zan yi in gama da ‘yan Bìndìgà>>Pastor Adegboye Gabriel Olabisi 

Ina da addu’ar da zan yi in gama da ‘yan Bìndìgà>>Pastor Adegboye Gabriel Olabisi 

Duk Labarai
Pastor Adegboye Gabriel Olabisi na cocin Worksword of God Church ya bayyana cewa ta hanyar karfin da Allah ya bashi, yana da addu'ar da zai yi wadda zata gama da 'yan Bindiga. Worksword of God Church dai a baya ya hakaito cewa, Bola Ahmad Tinubu zai zama shugaban Najeriya tun kamin ya zama. Kuma yakan bayyana abubuwa da yake tunanin zasu faru nan gaba
Kuma Dai:Kalli Bidiyon, Bayan Sanata Akpabio da Reno Omokri, Sanata Natasha tace akwai wani minista shima da ya nemeta da làlàtà

Kuma Dai:Kalli Bidiyon, Bayan Sanata Akpabio da Reno Omokri, Sanata Natasha tace akwai wani minista shima da ya nemeta da làlàtà

Duk Labarai
A yayin da ake tsaka da zargin da Sanata Natasha Akpoti kewa kakakin majalisar dattijai, Sanata Godswill Akpabio na cewa yana son lalata da ita, An gano cewa ta tabata zargin tsohon hadimin shugaban kasa, Reno Omokri da irin wannan zargi. Saidai duk ba'a gama da wannan ba, har ila yau, Wani bidiyon Sanata Natasha Akpoti ya bayyana inda aka jita tana kuma zargin wani minista da neman yin lalata da ita. https://www.youtube.com/watch?v=olzYFAEd6EM?si=y29YEntQW7Mmle9V Saidai a wannan karin bata fadi sunan Ministan ba. Kalli Bidiyon anan
Bamu yadda ba zamu je kotu, Kungiyar Kiristoci kan hutun Ramadan da jihohin Arewa suka bayar a makarantu

Bamu yadda ba zamu je kotu, Kungiyar Kiristoci kan hutun Ramadan da jihohin Arewa suka bayar a makarantu

Duk Labarai
Kungiyar Kiristocin Najeriya ta ce bata yadda ba kuma ta yi Allah wadai da kulle makarantu da jihohin Bauchi, Katsina, Kano, da Kebbi suka yi saboda zuwan Ramadana. A sanarwar da ya fitar ranar Lahadi a Abuja, shugaban CAN, Archbishop Daniel Okoh ya bayyana cewa wannan mataki zai kawo koma baya ga ci gaban ilimi da hadin kai a Najeriya. Kungiyar tace kulle makarantun zai taba harkar ilimi wadda 'yanci ne na dan adam kuma sannan ginshiki ne na ci gaban al'umma kuma hakan zai kara tabbatar da koma baya ga harkar ilimi a jihohin. Yace ba'a tuntubesu dan neman shawara kamin daukar wannan mataki ba kasancewa akwai kiristoci a wadanan jihohin. Yace kuma wani abin mamaki shine kasashen da musulmai suka fi yawa irin su UAE, da Saudi Arabia da sauransu duk basu kulle makarantu ba saida...
”Yan Bìndìgà sun kashe daliba Maryam da suka sace a jami’ar jihar Zamfara duk da karbar kudin Fansa

”Yan Bìndìgà sun kashe daliba Maryam da suka sace a jami’ar jihar Zamfara duk da karbar kudin Fansa

Duk Labarai
'Yan Bindiga da suka yi garkuwa da daliba a jami'ar jihar Zamfara, Zarah Abubakar Shehu sun kasheta duk da karbar kudin fansa. An sace tane tare da 'yan uwanta biyu a ranar Nov. 3, 2024 inda suka nemi Naira Miliyan 35 a matsayin kudin fansa, saidai daga baya an koma Miliyan 10 bayan tattaunawa. Saidai bayan da aka kai kudin fansar sun rike Zarah inda suka ce sai an sake kai musu mashina 4 da Engine oil. Saidai bayan da aka kai musu, sunce Zahra ta rasu har sun binneta.