Ba za mu bari PDP ta nutse da mu ba – Sanatocin Kebbi
Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi, waɗanda suka sauya sheƙa daga babbar jam'iyyar adawa ta PDP zuwa APC mai mulki sun ce sun fita daga jam'iyyar ce sanadiyyar rikice-rikice na cikin gida.
A jiya Talata ne shugabancin majalisar dattajai ya tabbatar da sauya shekar sanatocin wato Sanata Adamu Aliero mai wakiltar Kebbi ta tsakiya da Yahaya Abdullahi mai wakilartar Kebbi arewa da kuma Garba Maidoki mai wakiltar Kebbi ta kudu.
Sanatocin sun ce sun fice daga jam'iyyar ne saboda rikice rikicen cikin gida da suka yi wa jam'iyyar PDP katutu.
Daya daga cikinsu, Sanata Yahaya Abdullahi ya shaida wa BBC cewa a bayyane take tun bayan zaɓen 2023, jam'iyyar PDP ta shiga ruɗani da rikici kala-kala, kuma har kawo yanzu babu alamun jam'iyyar tana ɗaukar matakin gyara matsalolin n...







