Saturday, February 21
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Dansandan Najeriya ya manto Bìndìgàrsà a gidan giya bayan da yayi mankas

Dansandan Najeriya ya manto Bìndìgàrsà a gidan giya bayan da yayi mankas

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Osun na cewa, Wani Dansanda ya manto Bindigarsa a gidan giya a jihar bayan da yayi Mankas da giya. Rahoton yace lamarin ya farune a Osogbo babban birnin jihar ta osun. An bayyana sunan dansandan da wannan lamari ya faru dashi da sunan Inspector Monday. Saidai yayi karyar cewa ya mayar da Bindigar wajan da suke ajiye makamai, saidai da aka bincika an gano karya yake. Hakan na zuwane yayin da ake tuhumar manyan 'yansandan Najeriya kan batan Bindigu da yawa.
Kai ba karamin yaro bane, ya kamata ka sawa Zuciyarka dangana akan maganar rasa mukamin Minista>>Tinubu ya gayawa El-Rufai

Kai ba karamin yaro bane, ya kamata ka sawa Zuciyarka dangana akan maganar rasa mukamin Minista>>Tinubu ya gayawa El-Rufai

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gayawa tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya hakura da maganar rasa mukamin minista wadda an yi tun tuni. Ya bayyana hakane ta bakin kakakinsa, Bayo Onanuga inda yace El-Rufai sai raki yake kamar wani karamin yaro da aka kwacewa biredi. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na ChannelsTV. Onanuga yace kamata yayi El-Rufai ya sakawa ransa dangana ya bar maganar rasa mukamin ministan da yayi. Onanuga yace yana tausayawa El-Rufai dan ya ga Alamar lamarin ya bata masa rai sosai. A jiya ne dai El-Rufai a hirarsa da Arise TV ya bayyana cewa, Tinubu ne ya ki bashi minista ba Majalisa ce ta ki amincewa dashi ba.
Tinubu sai yayi 8 kamin ya sauka, ‘yan Bakin ciki saidai su mutu>>APC

Tinubu sai yayi 8 kamin ya sauka, ‘yan Bakin ciki saidai su mutu>>APC

Duk Labarai
Wani jigo a Jam'iyyar APC me mulki, Tolu Bankole wanda yana cikin kwamitin gudanarwa na Jam'iyyar ya bayyana cewa babu gurbi a Aso Rock sai shekarar 2031 bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kammala wa'adinsa na mulki. Ya bayyana cewa, shugaba Tinubu ba zai sauka daga mulki ba sai ya cika wa'adin da kundin tsarin mulki ya bashi damar yi na shekaru 8. Da yake magana akan hadaka da ake samu tsakanin 'yan adawa da niyyar kayar da gwamnatin Tinubu a shekarar 2027, yace yana baiwa 'yan adawar shawarar dama kada su bata kudadensu da lokutansu. Yace Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi ayyuka da suka amfani mutane sosai sannan suka habaka tattalin arzikin Najeriya.
Barawo Ya Sace Wayar Wannan Malamain, Bayan Kwana Biyu Kuma Barawon Ya Mutu, Shine Ake Zargin Malamain Da Hannu A Mutuwar Barawon

Barawo Ya Sace Wayar Wannan Malamain, Bayan Kwana Biyu Kuma Barawon Ya Mutu, Shine Ake Zargin Malamain Da Hannu A Mutuwar Barawon

Duk Labarai
BA FADA DA MALAM BA… Barawo Ya Sace Wayar Wannan Malamain, Bayan Kwana Biyu Kuma Barawon Ya Mutu, Shine Ake Zargin Malamain Da Hannu A Mutuwar Barawon Saidai a hirar da aka yi da Malamin ya ce shi ba shida hannu a mutuwar domin hasalima ya yafewa barawon wayarsa da ya sace masa. Malamin ya kuma kara da cewa duk wanda ya ce shine ya kashe barawon wayan nasa, to shima ya jira nasa. Me za ku ce?
Taufa Kalli Yanda wani dan Kripto ya lalata kwamfutarsa da sauran kayan amfaninsa saboda haushin Kasuwa ta lalace, yace ya sayar da komai

Taufa Kalli Yanda wani dan Kripto ya lalata kwamfutarsa da sauran kayan amfaninsa saboda haushin Kasuwa ta lalace, yace ya sayar da komai

Duk Labarai
Wani Dan Kripto ya bayyana rashin jin dadinsa da yanda kasuwar ta lalace a yanzu inda ya bayyana cewa ya sayar da duk wani abu na Cryptocurrency daya mallaka. Ba wannan kadai ba kuma ya sanar da lalata Kwamfutatsa da sauran kayan da yake amfani dasu. Wasu sun bashi baki inda akai masa jaje yayin da wasu suka ce basu ma yadda dashi ba.
Wata mata me suna Salamatu ta kkàshe Mijinta a jihar Bauchi ta hanyar daba masa wuka

Wata mata me suna Salamatu ta kkàshe Mijinta a jihar Bauchi ta hanyar daba masa wuka

Duk Labarai
Wata mata a jihar Bauchi me suna Salamatu Danjuma me kimanin shekaru 25 ta kashe mijinta ta hanyar daba masa wuka. Lamarin ya farune a garin Nadago dake karamar hukumar Tafawa Balewa. Kakakin 'yansandan jihar, Ahmed Wakil ya tabbatar da faruwar lamarin ranar Litinin inda yace rikici kan rikon diyarsu ne ya jawo fadan da ya kai ga matar ta dabawa mijinta wuka. An kai mijin Asibiti inda likitoci suka tabbatar da ya mutu. Kwamishinan 'yansandan jihar,Auwal Mohammed ya bayar da umarnin yin bincike sosai akan lamarin.
Dalibin jami’a ya nutse ya mutu a ruwa bayan da aka saka masa Naira 300 idan ya tsallake ruwan da iyo

Dalibin jami’a ya nutse ya mutu a ruwa bayan da aka saka masa Naira 300 idan ya tsallake ruwan da iyo

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, dalibin jami'ar Federal University, Otuoke jihar Bayelsa ya nutse a ruwa bayan da suka yi caca shi da abokansa. Dalibin sun yi gaddama da abokansa kan cewa, ba zai iya tsallake wani ruwa bane da iyo inda shi kuma yace zai iya. Anan ne sai suka saka Naira Dari uku kowannensu shi da abokansa. Ya shiga ya fara iyo a cikin ruwan sai suka ga ya nutse, har zuwa lokacin hada wannan rahoto ba'a gano gawarsa ba. Rahoton jaridar Punchng ya bayyana cewa an yi kokarin tuntubar hukumar makarantar dan jin ta bakin kakakin makarantar Ms Mercy Ekott, saidai an ta kiran wayarta amma taki dagawa. An kuma tuntubu kakakin 'yansandan jihar, Mr Musa Mohammed inda yace bai san da maganar ba.
An kama matashi da ya kkàshè Budurwarsa

An kama matashi da ya kkàshè Budurwarsa

Duk Labarai
Mahukunta a jihar Legas sun kama wani mutum me suna Gbolahan Adebayo bida zargin kashe budurwarsa. Adebayo dan shekaru 23 ya daki budurwarsa me shekaru 25 har ta mutu. Lamarin ya farune a ranar 21 February 2025 kamar yanda Daily Post ta ruwaito. Kakakin 'yansandan jihar, Benjamin Hundeyin ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace abin ya farune a Ijedodo, Isheri-Osun dake jihar. Wani makwabci daya shaida lamarin yace ya ji Adebayo na dukan budurwar tasa kuma da aka leka aka tarar bata motsi, saidai zuwa yanzu ba'a san dalilin da yasa ya kashe budurwar tasa ba. Tuni dai aka kai ta Asibiti inda likitoci suka tabbatar da ta mutu.
Haduwar Mawakiyar Najeriya, Ayra Starr da shahararriyar me yin fina-finan bàtsà Mìa Khàlìfà ya jawo cece-kuce

Haduwar Mawakiyar Najeriya, Ayra Starr da shahararriyar me yin fina-finan bàtsà Mìa Khàlìfà ya jawo cece-kuce

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Tauraruwar Mawakiyar Najeriya, Ayra Starr ta hadu da shahararriyar me fina-finan batsa, watau Mia Khalifa. Bidiyon haduwarsu suna hira ya karade kafafen sada zumunta inda wasu ke tambayar me ya hadasu? Mia Khalifa dai wadda asalinta 'yar kasar Lebanon ce ta bayyana daina yin fina-finan batsa, inda ta koma shafin Onlyfan wanda saidai idan mutum nason ta mai bidiyon ta tsirara ya biya kudi ta masa.
Bidiyo:Na Tuba na daina Yada Badala>>Inji ‘Yar Tiktok, Shalele

Bidiyo:Na Tuba na daina Yada Badala>>Inji ‘Yar Tiktok, Shalele

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok da ta shahara sosai wajen yada badala da maganganun batsa Shalele ta bayyana cewa ta tuba. Shalele wadda har bidiyoyinta tsirara sun yadu sosai tace daga yau ta daina duk wani na ba daidai ba da ya sabawa Addini da Al'ada. https://www.tiktok.com/@drshalele2/video/7473392723249106231?_t=ZM-8uCdD1ruVtv&_r=1 Da yawa sun jinjina mata kan wannan mataki data daukarwa rayuwarda.