Friday, February 20
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Hotunan Ango da Amarya da suka jawo cece-kuce

Kalli Hotunan Ango da Amarya da suka jawo cece-kuce

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wadannan hotunan wasu sabbin ma'aurata ne da suka jawo cece-kuce a kafafen sada zumunta musamman saboda karamin jiki da amaryar ke dashi. Saidai Binciken da hutudole.com yayi, ya fahimci cewa matar shekarunta 30 kuma har ma ta kammala jami'a, kawai dai bata da jikin girma ne. Muna musu fatan zaman lafiya da zuri'a dayyiba.
Dalilin da yasa na kkàshè babban abokina kuma aminina wanda muka taso tare tun muna yara watau Mamman Batsa>>IBB ya magantu

Dalilin da yasa na kkàshè babban abokina kuma aminina wanda muka taso tare tun muna yara watau Mamman Batsa>>IBB ya magantu

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasar mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida yayi bayanin dalilin da yasa ya kashe babban abokinsa da suka taso tare watau Mamman Batsa. Babbangida yace yana sane da cewa, Mamman Batsa tun suna yara yana kishi da ci gaban da yake samu, yace amma duk da haka ko da ya zama shugaban kasa, sai da ya bashi ministan babban birnin tarayya Abuja, duk da yake cewa ba tare dashi akawa Buhari juyin mulki ba. Babangida yace ko da suna makaranta da aka bashi Shugaban dalibai, Mamman Batsa bayawa umarninsa biyayya inda yakan rika ce masa ai ba wani abun azo a gani bane dan mutum ya zama shugaban dalibai. Yace hakanan da suka shiga aikin soja ma ya rika masa hassada. Yace A lokacin da yake shugaban kasa, bincike ya tabbatar da cewa Mamman Batsa ya shirya kifar da gwamna...
Farashin Giya, dana taba sun kara tsada fiye komai a Najeriya>>NBS

Farashin Giya, dana taba sun kara tsada fiye komai a Najeriya>>NBS

Duk Labarai
Hukumar Kididdiga ta kasa, NBS ta bayyana cewa, farashin lemun kwalba, dana giya, dana taba dana sauran kwayoyi ne yafi kowane tashi a cikin kayan da ake amfani dasu a Najeriya. Farashin wadannan kayayyaki kamar yanda NBS ta bayyana ya tashi da kaso 14.80 a cikin watan Janairu da ya gabata. NBS tace kayan da suka fi tsada na biyu shine farashin kudin haya da na cin abinci a gidajen cin abinci a fadin kasarnan wanda ya tashi da kaso 14.14. Abinda ke biye musu shine farashin kayan sawa, da tafiye-Tafiye, da takalma, wanda suma suka yi tashi sama.
Watanni 7 bayan da Kotun koli tace a rika baiwa kananan hukumomi kudadensu kai tsaye ba tare da sun bi ta hannun gwamnoni ba har yanzu ba’a aiwatar da hukuncin ba

Watanni 7 bayan da Kotun koli tace a rika baiwa kananan hukumomi kudadensu kai tsaye ba tare da sun bi ta hannun gwamnoni ba har yanzu ba’a aiwatar da hukuncin ba

Duk Labarai
Watanni 7 kenan tun bayan da kotun koli ta yi hukunci inda tace a daina baiwa gwamnoni kudaden kananan hukumomi inda tace a rika baiwa kananan hukumomin kudadensu kai tsaye. Saidai har yanzu gwamnatin tarayya bata fara aiwatar da wannan hukunci ba, wanda wasu masana na ganin hakan kin girmama bangaren shari'a ne ganin cewa kotun koli itace kotu mafi girma a kasarnan. Dama dai tun a wancan lokaci, Gwamnoni sun shigar kara inda suka nemi dakatar da hukuncin amma basu yi nasara ba. A ranar July 11, 2024 ne kotun kolin karkashin jagorancin me shari'a Lateef Fagbemi SAN ta yi wannan hukunci. Gwamnatin tarayya a kokarin kawo tsaiko wajan aiwatar da wannan hukunci ta baiwa gwamnatocin jihohi watanni 3 su gudanar da zabukan kananan hukumomi dan fara aiwatar da wannan doka amma shiru ka...
‘Yan Fafutuka na kasashen Yarbawa sun bukaci a kama tsohon shugaban kasa, Janar Babangida a Hukuntashi

‘Yan Fafutuka na kasashen Yarbawa sun bukaci a kama tsohon shugaban kasa, Janar Babangida a Hukuntashi

Duk Labarai
Da yawan 'yan fafutuka na jihohin yarbawa sun nemi da a kama tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida a hukuntashi. Wasu daga cikinsu sun ce a zamanin mulkinsa ya azabtar dasu da iyalansu ya jefa rayuwarsu cikin rashin tabbas. A zamanin mulkin tsohon shugaban kasar da ya faru a tsakanin shekarun 1985 zuwa 1993 an gudanar da zaben Abiola wanda janar Babangida ya soke. Wannan ya jawo hargitsi a wancan lokacin wanda har sai da aka kashe mutane akalla 100, kamar yanda rahotanni suka bayyana. An kuma kama mutane da yawa saboda fitowa zanga-zanga musamman dan nuna rashin amincewa da soke zaben, daga cikin wadanda aka kama akwai Chief Gani Fawehinmi, Alao-Aka-Bashorun, Femi Falana, SAN, Femi Aborisade, Debo Adeniran, Kunle Ajibade. Dan hakane suka hada baki suka ce ba...
Tirr: Gwamna a kasar Amurka ya nemi a daina cewa uwa mahaifiya, a rika ce mata ma’ajiyar Maniyyi

Tirr: Gwamna a kasar Amurka ya nemi a daina cewa uwa mahaifiya, a rika ce mata ma’ajiyar Maniyyi

Duk Labarai
Gwamnan jihar Wisconsin ta kasar Amirka, Tony Evers ya nemi a canja sunan uwa a daina kiranta da mahaifiya a rika kiranta da ma'ajiyar Maniyyi. Ya bayyana hakane a cikin kasafin kudin da ya kai majalisar jiharsa inda ya kuma bukaci a canja sunan mahaifi da mata da miji duka. Saidai da yawan 'yan kasar Amurkar basu yi na'am da wannan shawara tasa ba inda suka rika sukarsa da cewa wannan cin zarafin mahaifiyane.
Mummunan hadari yayi sanadiyyar mùtùwàr Mutane 12, wasu sun jikka a jihar Naija

Mummunan hadari yayi sanadiyyar mùtùwàr Mutane 12, wasu sun jikka a jihar Naija

Duk Labarai
Wani mummunan Hadarin da ya faru a jihar Naija yayi sanadiyyar mutuwar mutane 12 inda wasu kuma suka jikkata. Lamarin ya farune akan titin Agaie zuwa Lapai. Kwamandan hukumar kiyaye hadura ta jihar, FRSC, Kumar Tsukwam ya tabbatarw da manema labarai hakan a sanarwar da ya fitar ranar Asabar a Minna. Yace har yanzu ma'aikatansa na wajan da hadarin ya faru inda yace zasu tattaro bayanai su bayar game da hadarin. Wani da ha shaida yanda abin ya faru, ya gayawa majiyarmu cewa, 3 daga cikin wadanda suka mutu 'yan gida dayane. Sannan sun ce hadarin ya farune a yayin da wata motar Bas ke tafiya daga Minna zuwa Katcha ta yi taho mu gama da wata trela a daidai kauyen Jippo dake kusa da Mashina. Wanda suka jikkata ciki hadda direban suna karbar kulawa a asibitin Lapai General Hospi...
Kalli Bidiyon yanda hukumar NAFDAC ta kama Kwandam(Kwaroron Roba) wanda ya lalace da ake sayarwa da mutane shi

Kalli Bidiyon yanda hukumar NAFDAC ta kama Kwandam(Kwaroron Roba) wanda ya lalace da ake sayarwa da mutane shi

Duk Labarai
A wani abin mamaki da ya faru, an kama wasu dake sayar da kwaroron roba da ya lalace. Suna canja masa mazubine da kuma shekarar da ya kamata ya lalace inda suke sake sayar dashi kamar sabo. Kuma shi wannan kwaroron roba, hukumar kasar Amurka, USAID ce ta bayar dashi kyauta. https://www.youtube.com/watch?v=CpJh-x9vvVk Masana ilimin lafiya sun bayyana cewa, amfani da kwaroron roba da ya lalace zai iya sawa ya huje yayin da ake amfani dashi wanda hakan ka iya kaiwa ga daukar cikin da ba'a shirya ba da muna kamuwa da cutukan da ake dauka a wajan jima'i. Tuni dai hukumomi a ma'aikatar lafiya suka sanar da daukar matakan fara binciken dan gano masu aikata irin wannan ta'asa.
Kamfanin sadarwar Airtel ya sanar da tafka asarar Dala Miliyan $344 a kasuwancin sayar da data

Kamfanin sadarwar Airtel ya sanar da tafka asarar Dala Miliyan $344 a kasuwancin sayar da data

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kamfanin sadarwa na Airtel ya sanar da tafka asarar Dala Miliyan $344 a wajan kasuwancin sayar da data. Kamfanin yace ta tafka asarar a watanni 9 da suka gabata wanda suka kare a karshen watan Disamba na shekarar 2024. A shekarar baya kamfanin ya samu kudin shiga daga kasuwancin sayar da data wanda suka kai dala miliyan $539. Hakan na faruwane yayin da yawan masu amfani da layin waya na Airtel suka karu wanda a yanzu sun kai Mutane Miliyan 56.6. Shugaban kamfanin, Dinesh Ba...