Shugabar hukumar tsaron Homeland Security ta kasar Amurka, Kristi Noem ta gamu da 'yan sane inda suka sace mata karamar jaka ta mata da ake cewa Purse.
Jakar dai na dauke da Dala $3000 da kuma katinta na aiki.
Hakanan an sace jakar ne a wani wajen cin abinci dake baban birnin kasar watau Washington DC.
Hakana Barawon ya kuma sace jakar dake dauke da magungunan matar.
Ta je gidan abincinne dan cin abinci da danginta a matsayin ranar Bikin Easter.
Darajar hannun jari a Amurka da kuma kuɗin ƙasar Dala, ta ƙara faɗuwa, bayan da Shugaba Trump ya sake nanata sukar da yake yi wa shugaban babban bankin ƙasar.
A wani saƙo da ya sanya a shafinsa na sada zumunta da muhawara na - Truth Social, Mista Trump ya kira, shugaban bankin Jerome Powell a matsayin babban mai asara, saboda ya ƙi rage yawan kuɗin ruwa.
Wannan matsala da ke ci gaba ta sake tasowa ne a wannan karon yayin da shugabanni da jagororin harkokin kudade suke nufar babban birnin Amurka - Washington domin halartar taron Babban Bankin Duniya, da kuma Asusun Bayar da Lamuni na duniya, IMF.
Shugaban kamfanin zuba jari na kamfanin Scharf Investments, Brian Krawez, ya yi bayani kan wannan hali na kara sulmiyowar darajar hannayen jari na Amurka da kuma darajar Dalar, bayan da Sh...
Kauyuka da yawa ne suke biyan 'yan Bindiga kudaden Haraji a jihar Zamfara dan kada su kai musu hari ko su yi garkuwa dasu.
A shekarar 2025 dinnan da muke ciki kawai, watau daga watan Janairu zuwa yanzu Mutanen jiha Zamfarar sun biya 'yan Bindiga jimullar Harajin Naira Miliyan 500, kamar yanda jaridar Daily Trust ta bayyana.
A watan Janairu kawai, marigayi dan Bindiga Isuhu Yellow, ya kakabawa mutanen kauyuka 25 harajin Naira Miliyan 172.7.
Hakanan shima Dogo Gide ya kakabawa kauyuka 23 Harajin Naira Miliyan 100.
Lamarin 'yan Bindiga dai na ci gaba da ta'azzara duk da ikirarin kokarin da gwamnati ke cewa tana yi.
Mutanen jihohin Katsina, Kano, da Jigawa na fuskantar matsi saboda karancin wutar lantarkin da suke samu inda a yanzu wutar awanni 2 kacal ake basu a yini.
Da yawan kananan 'yan kasuwa sun koka da cewa suna fuskantar matsala wajan gudanar da ayyukansu saboda rashin ko karancin wutar a wadannan jihohi.
Yawancin kasuwancin da wannan matsala tafi shafa sune Teloli, Masu sayar da kankara, mas cajin waya, masu sana'ar walda da sauransu.
Hukumar wutar dake kula da wadannan jihohi, (KEDCO) ta bayyana cewa an samu karancin wutar ne saboda gyare-gyaren da take dan inganta ayyukanta.
'
Yan kasuwar man fetur sun koka da sarar da suka tafka bayan da kamfanin mai na kasa NNPCL ya rage farashin man da yake sayarwa.
A Legas, NNPCL na sayar da litar man fetur din aka farashin Naira 880 kan kowace lita yayin da a Abuja kuma NNPCL din na sayar da man fetur din akan farashin 935 akan kowace lita.
Hakan na zuwane sati daya bayan da Dangote ya rage farashin man fetur din nasa.
A Legas, Farashin man fetur din na NNPCL yafi na Dangote Arha da Naira 10.
Saidai kamfanin na NNPCL ya baiwa 'yan kasuwar damar su sayar da tsohon man da suke dashi kamin fara amfani da sabon farashin.
Idan dai ana duba bunƙasar cocin Katolika ne wajen zaɓen fafaroma na gaba, da tabbas babu wani zaɓi illa daga Afirka.
Afirka ce ke da mabiya Katolika da suka fi ƙaruwa cikin sauri a duniya, inda suka ƙaru da kashi 3.31 cikin 100 a shekara biyu tsakanin 2022 da 2023. Alƙaluma na baya-bayan nan daga Fadar Vatican kashi 20 na mabiya Katolika ne ke zaune a Afirka.
A gefe guda kuma, nahiyar Turai ta fuskanci ƙaruwa mafi ƙanƙanta a wannan lokaci. Daga shekarar 1910 zuwa 2010, an samu raguwar mabiya ɗariƙar da sama da kashi 63, a cewar alƙaluman binicke na cibiyar Pew Research.
Nahiyar ta Turai da ake yi wa kallon cibiyar Kiristanci ta duniya, yanzu ta zama ɗaya daga cikin mafiya nisa da addini gaba ɗaya.
Duk da cewa har yanzu Katolika na da ƙarfi a nahiyar Latin Amurka, Ibanjilika na...
Rahotanni sun bayyana cewa yawan kayan da kamfanoni ke sayarwa a Najeriya sun ragu saboda mutane basu da kudin saye.
Kungiyar masu kamfanoni da masana'antu a Najeriya, MAN ne suka bayyana hakan.
Rahoton yace an samu karuwar kayan da ba'a sayarba zuwa kaso 87.5 wanda darajar kayan sun kai Naira Tiriliyan 2.14 a shekarar 2014.
Hakan ya nuna cewa yawan kayan da masana'antun basu siyarba ya karu idan aka kwatanta daga shekarar 2013 zuwa 2014.
Kayan da suka fi fama da wannn matsala sun hada dana abinci, da lemukan kwalba, da taba da kayan sawa da takalma da sauransu.
Tsohon sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir David Lawal ya bayyana cewa ba sai tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya goyi bayan dan takara ba kamij dan takar yayi nasara akan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba a shekarar 2027.
Ya bayyana hakane a hirar da jaridar Punchng ta yi dashi inda yace suna zuwa gurin Buhari ne a matsayinsa na babba dan sanar dashi abinda zasu yi ya saka musu Albarka.
Yace amma basa bukatar tsohon shugaban kasar ma ya shiga tafiyarsu dan suna da hankali da wayau sun san yanda zasu gudanar da al'amuransu.
Babachir yace Gwamnatin Tinubu bata son talakawa ne shiyasa take kokarin ganin ta sakasu a wahalar da zata kai su ga halaka.
Yace su kuma abinda suka fito dan karewa kenan talakawa da masu rauni.
Rahotanni sun bayyana cewa matakan da babban bankin Najeriya, CBN ya dauka dan rage yawan kudaden dake hannun 'yan Najeriya basu bayar da sakamakon da ake so ba.
Babban bankin Najeriya ya dauko matakai masu tsauri sosai dan ganin an rage yawan kudaden dake hannun mutane a Najeriya amma hakan bata samu ba.
Rahoton yace fiye da kaso 90 na tsabar kudin dake yawo a Najeriya na hannun mutanene basa cikin bankuna.
Wanda hakan ke kara nuna cewa mutane sun fi yadda da yin ciniki da kudin zahiri fiye da amfani da banki ko fasahar kasuwanci ta zamani.
Hakan na faruwa ne duk da kokarin gwamnati na karfafa gwiwar mutane wajan rage yawa amfani da tsabar kudi a yayin gudanar da kasuwanci.
Masana tattalin arziki dai sun bayyana cewa idan kudi suka yi yawa a hannun mutane, kayan masarufi za...