Tuesday, December 23
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Wani Malamin Addinin Islama daga kasar Yarbawa ya dauki hankula bayan da yace wai idan ka gayawa Saniya cewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi Wafati zaka ga Bàlà’i, ba zaka koma gida Lafiya ba

Wani Malamin Addinin Islama daga kasar Yarbawa ya dauki hankula bayan da yace wai idan ka gayawa Saniya cewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi Wafati zaka ga Bàlà’i, ba zaka koma gida Lafiya ba

Duk Labarai
Wani malamin Addinin Islama daga kasar Yarbawa ya dauki hankula bayan da yace wai idan mutum ya gayawa Saniya cewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yayi wafati zai ga bala'i ba zai koma gida Lafiya ba. Malamin a cewarsa wai Shanu basu san Annabi yayi wafati ba. https://twitter.com/AsakyGRN/status/1992651245262409903?t=4GXhdskTqsxpe45WCJa9QA&s=19 Dan fafutuka na kudu, VDM ya gwada inda ya je ya samu wasu shanu ya gaya musu amma babu abinda ya faru dashi. https://twitter.com/Mautiin01/status/1993248995842662582?t=Gf9RXfSp59Z6Tf0VV5WGkg&s=19
Fadar shugaban kasa tace ba zata yafewa Peter Obi ba saboda cewar da yayi da shine shugaban kasa zai amince Amirka ta kawo Khari Najeriya

Fadar shugaban kasa tace ba zata yafewa Peter Obi ba saboda cewar da yayi da shine shugaban kasa zai amince Amirka ta kawo Khari Najeriya

Duk Labarai
Fadar Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta bayyana cewa, ba zata yafewa Peter Obi ba saboda kalaman da yayi na amincewa da cewa shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya kawo Hari Najeriya. Me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a rubutun da yayi a shafinsa na X inda yace ba zasu amince da kawo harin na Trump ba. Peter Obi yace kamar mutum ne da iyalansa na fama da yunwa kawai sai wani ya kawo musu abinci, yace ai kamata yayi ya amince. Yace to Najeriya abinda take bukata ne Amurka tace zata kawo mata ai kamata yayi kawai ta amince.
Da Duminsa: Fadar Shugaban kasa tace Sojoji da DSS sun kira Tshàgyèràn Dhàjì suka ce su saki mutanen da suka yì Ghàrkùwà dasu a coci kuma sun sake su din

Da Duminsa: Fadar Shugaban kasa tace Sojoji da DSS sun kira Tshàgyèràn Dhàjì suka ce su saki mutanen da suka yì Ghàrkùwà dasu a coci kuma sun sake su din

Duk Labarai
Fadar Shugaban kasa ta tabbatar da cewa, DSS da sojoji sun kira 'yan Bìndìgà da suka yi garkuwa da mutanen cocin Eruku, dake karamar hukumar Ekiti a jihar Kwara suka ce su sakesu. Me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a hirar da aka yi dashi a Arise TV. Yace Jami'an tsaron sun kira 'yan Bindigar suka ce su saki mutanen da suka sace a cocin kuma suka sakesu saboda sun san rashin sakinsu ko rashin yiw Gwamnati biyayya sakamakon da zai zo musu dashi. Yace mataki na gaba da jami'an tsaron zasu dauka wannan kuma sirri ne. Hakanan yace a lokuta da dama jami'an tsaron kan samu bayanin inda 'yan Bindigar suke amma saboda gudun kada harin da zasu kai ya shafi wadanda ake rike dasu shiyasa basu cika Afkawa Tshàgyèràn Dhàjìn ba.
Kalli Bidiyo: Gfresh ya wallafa Bidiyo suna soyewa shi da Sadiya Haruna, Wasu sun ce dan ya baiwa matarsa Haushi ne

Kalli Bidiyo: Gfresh ya wallafa Bidiyo suna soyewa shi da Sadiya Haruna, Wasu sun ce dan ya baiwa matarsa Haushi ne

Duk Labarai
An ga Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin tare da tsohuwar matarsa suna Shekye aya a cikin mota a wani Bidiyo da ya walafa. Gfresh ya rika Taba Sadiya Haruna a habarta sannan yana kwanciya a jikinta. Wasu dai sun ce yana yin hakanne dan ya baiwa matarsa, Maryam Haushi ne. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7576394652706671880?_t=ZS-91gmKjiSyvI&_r=1
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Ji Yanda Wani me suna John Ya Hàllàqà wani Almàjìrì a jihar Kebbi

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Ji Yanda Wani me suna John Ya Hàllàqà wani Almàjìrì a jihar Kebbi

Duk Labarai
Ana zargin Wani me suna john da yiwa wani Almajiri yankan Rhago a jihar Kebbi. Malamin Almajirin me suna Sani ya bayar da labarin yanda lamarin ya kasance inda yace ya kammala sallar Asubahi sai yara suka shiga suka gaya masa. Yace yaran sun so su dauki doka a hannu amma sai yaje ya kira 'yansanda. https://twitter.com/DanKatsina50/status/1992975711380881644?t=1Ck-luZv8G_x2dWql4C9-Q&s=19
Idan ba Gwamnatice ta daure mana Gìndy muke abìndà muke ba Allah ya Tsynè min Allbarka>>Inji Wani Tshàgyèràn Dhàjì

Idan ba Gwamnatice ta daure mana Gìndy muke abìndà muke ba Allah ya Tsynè min Allbarka>>Inji Wani Tshàgyèràn Dhàjì

Duk Labarai
Wani bafulatani wanda dan Bindiga ne ya bayyana cewa Gwamnati ce ta daure musu gìndy suke abinda suka ga dama na ta'addanci. Bidiyon bafulatanin tsohon Bidiyon ne amma saboda yawaitar hare-haren 'yan Bìndìgà yasa ake ta kara yadashi a kafafen sada zumunta. Yace Saniya bata Haifar Bindiga. https://twitter.com/OurFavOnlineDoc/status/1992833250264219726?t=8FDH9pL-LZUei7DkqMZVOA&s=19
Fàrgàbàr tsàrò ta faru a makarantar Government Girls College, Maiduguri

Fàrgàbàr tsàrò ta faru a makarantar Government Girls College, Maiduguri

Duk Labarai
Rahotanni daga makarantar Government Girls College, Maiduguri dake jihar Borno sun bayyana cewa, An samu fargabar tsaro a tsakanin daliban makarantar. Rahotanni sun ce lamarin ya farune da daren ranar Litinin inda Daliban suka suka fita da gudu suna cewa sun ga wasu sun shiga makarantar. Saidai Hukumomin makarantar sun bayyana cewa jita-jita ce kawai ta faru sun yi bincike babu wata fargabar tsaro a makarantar. Hakanan hukumar 'yansanda ta jihar ma ta tabbatar da cewa babu wata matsalar tsaro da ta faru a makarantar. Hakan na zuwane a yayin da ake fama da satar dalibai a makarantu daban-daban na Arewa.
‘Yan damfarar Yanar gizo su fi kowane irin bata gari yiwa Najeriya illa ta fannin tattalin arziki>Inji EFCC

‘Yan damfarar Yanar gizo su fi kowane irin bata gari yiwa Najeriya illa ta fannin tattalin arziki>Inji EFCC

Duk Labarai
Hukumar yaki da Rashawa da cin hanci a Najeriya, EFCC ta bayyana cewa, 'yan damfarar yanar gizo, watau Yahoo Boys sun fi kowane irin bata gari yiwa Najeriya illa. Me magana da yawun Hukumar, Dele Oyewale ne ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai. https://twitter.com/NigeriaStories/status/1993002019670667546?t=oGgnUHsBIz-zPzaTsFhpeA&s=19
Duk Wata cefanen Dubu dari shida nakewa matata da kasuwanci na saka kudin da yanzu naci riba>>Inji Gfresh Al-amin

Duk Wata cefanen Dubu dari shida nakewa matata da kasuwanci na saka kudin da yanzu naci riba>>Inji Gfresh Al-amin

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya bayyana cewa, Duk wata cefanen Naira Dubu dari shida yake wa matarsa. Yace amma yanzu idan shi kadai ne dubu dari da hamsin ta isheshi. Ya bayyana cewa kudaden da yake kashewa matar tasa da kasuwanci ya sakasu da ba karamar riba zasu kawo masa ba. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7576326800993832199?_t=ZS-91fs2JLOXOD&_r=1 Gfresh ya bayyana hakane bayan rabuwarsa da matarsa inda ya mata saki daya biyo bayan zuwa wajan tsohuwar matarsa, Sadiya Haruna da yayi.
Da Duminsa: Kasar Ingila ta ki amincewa da Bukatar Gwamnatin Najeriya ta a dawo da Ike Ekweremadu Najeriya ya kammala zaman gidan yarinsa anan

Da Duminsa: Kasar Ingila ta ki amincewa da Bukatar Gwamnatin Najeriya ta a dawo da Ike Ekweremadu Najeriya ya kammala zaman gidan yarinsa anan

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Ingila na cewa, kasar ta ki amincewa Najeriya ta dawo da Sanara Ike Ekweremadu Najeriya ya kammala zaman gidan yarinsa anan. Sanata Ike Ekweremadu na zaman gidan yari a kasar Ingila ne bayan da aka kamashi da laifin safarar dan adam da kuma cire sassan jikin dan adan ba tare da izini ba. Gwamnatin tarayya ta aike da tawaga ta musamman zuwa kasar Ingila dan ta roki kasar a dawo da Sanata Ike Ekweremadu ya ci gaba da zaman yarinsa a Najeriya. Saidai kasar tace bata yadda ba.