Wednesday, February 18
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Wallahi Mutuwar Aure Bàlà’ì Ne Ga Mata, Ko Da A Ce Mijìnki Dukanki Yake Gwamma Ki Yi Hakuri Ki Zauña, Inji Mansura Isah

Wallahi Mutuwar Aure Bàlà’ì Ne Ga Mata, Ko Da A Ce Mijìnki Dukanki Yake Gwamma Ki Yi Hakuri Ki Zauña, Inji Mansura Isah

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohuwar jarumar Kannywood, Mansurah Isah, wadda tsohuwar matar Sani Musa Danja ce, ta bayyana hakan cikin wani bidiyo da ta wallafa. A cikin bidiyon ta bayyana yadda mata ke shiga mawuyacin hali bayan mutuwar aurensu. Ta shawarci mata da su kasance masu haƙuri a gidajensu na aure tare da gujewa duk wani abu da ka iya kawo musu ɓaraka da mazajensu. Ta yi gargaɗin cewa babu komai a rayuwar zawarci sai tarin baƙin ciki da da-na-sani. Me za ku ce?
Tsaffin sojoji da suka yi ritaya sun yi zanga-zangar rashin biyansu albashi

Tsaffin sojoji da suka yi ritaya sun yi zanga-zangar rashin biyansu albashi

Duk Labarai
Tsaffin sojoji da suka yi ritaya ranar Talata sun kai kujeru da rumfa a kofar fishin ma'ikatar kudi dake Abuja inda suka yi zaman dirshan suka bukaci a biyasu hakkokinsu. Dama dai a watan Disamba daya gabata, sojojin sun yi irin wannan zanga-zanga ta neman hakkinsu. Watanni da yawa sun shude inda ake gayawa tsaffin sojojin cewa, babu kudin da za'a biyasu hakkokin nasu. Bayan zanga-zangar da suka yi a watan Disamba, an biyasu kaso 50 cikin 100 na hakkokin nasu inda aka musu alkawarin biyan suran amma sunce har yanzu shiru.
Ana barazana ga rayuwata – Obi

Ana barazana ga rayuwata – Obi

Duk Labarai
Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a Jam'iyyar Labour a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ce ana yi wa rayuwarsa barazana saboda sukar gwmnatin Shugaban Ƙasa Tinubu da ya yi a saƙonsa na sabuwar shekara. A saƙon nasa na sabuwar shekarar, Obi ya bayyana cewa Najeriya na fama da taɓarɓarewar tattalin arziki da rashin tsaro da rashin ingantaccen kiwon lafiya. A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya ce, "shin na wuce iyaka? na yi wannan tambayar ce saboda ana yi wa rayuwata da ta iyalina barazana saboda jawabin da na yi na sabuwar shekara. Bayan barazanar kuma, wani mai suna Mr Felix Morka ya zarge ni da wuce iyaka, sannan ya yi barazanar zan ɗanɗana kuɗata," in ji shi. Obi ya ƙara da cewa idan har da gaske ya karya doka, a nuna masa, inda ya ƙara da cewa, "amma ba zan daina faɗin ga...
Aƙalla mutum 95 sun ràsù a girgizar ƙasa a China

Aƙalla mutum 95 sun ràsù a girgizar ƙasa a China

Duk Labarai
Wata mummunar girgizar ƙasa ta afku a kusa da iyakar Tibet da Nepal. Aƙalla mutum 95 ne aka tabbatar da mutuwarsu, sannan sama da 130 sun jikkata a girgizar, wadda ta afku a ranar Talata. Girgizar ta kuma ƙetara zuwa yankin Nepal da ke ƙasar Indiya, wanda ke maƙwabtaka da Tibet na ƙasar China. Girgizar ƙasar ta lalata gine-gine a birnin Shigatse na Tibet, lamarin da ya sa jama'a su riƙa kwararowa kan tituna domin tsira. Tuni sojojin ƙasar suka fara aikin ceto, inda suka aika jirage marasa matuƙa zuwa wani yanki mai nisa a kusa da tsaunin Everest.
An fara bincike kan harin da B0k0 Hàràm ta kai kan sojoji a Borno

An fara bincike kan harin da B0k0 Hàràm ta kai kan sojoji a Borno

Duk Labarai
Rundunar tsaron Najeriya ta ƙaddamar da bincike kan harin da ƴan Boko Haram suka kai wa sojojin ƙasar a sansaninsu da ke jihar Borno a arewa maso gabashin ƙasar. Rahotanni sun ce harin na Boko Haram ya yi ajalin aƙalla sojojin Najeriya shida a sansanin sojojin da ke Damboa a ranar Lahadi, kamar yadda kafar AFP ta ruwaito, inda ta ce tsagin Boko Haram na ISAWP ne suka kai harin. Kakakin rundunar tsaron Najeriya, Manjo Janar Edward Buba ya tabbatar da harin, amma bai bayyana adadin waɗanda aka kashe ba. Sai dai ya ƙara da ecwa, "mun fara bincike kan lamarin. Za mu fitar da sanarwa game da harin nan kusa," kamar yadda ya bayyana wa BBC.
Gwamnan jihar Bauchi ya sallami Kwamishinoni 5

Gwamnan jihar Bauchi ya sallami Kwamishinoni 5

Duk Labarai
Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad ya sallami kwamishinoni 5 daga gwamnatinsa a kokarin yin garambawul da inganta tafiyar da mulki. Me magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado ne ya bayyana haka a sanarwar da ya fitar ranar Talata. Kwamishinonin da aka sauke sune; Dr. Jamila Dahiru (Education) Abubakar Bununu (Internal Security and Home Affairs) Usman Danturaki (Information and Communication) Prof. Simon Yalams (Agriculture) Yakubu Hamza (Religious Affairs and Societal Reorientation) Gwamnan yace ya godewa kwamishinonin bisa gudummawar da suka bayar wajan nasarorin da aka samu a gwamnatinsa. Sannan ya bayar da sunayen sabbin kwamishinoni 8 ga majalisar jihar dan tantancewa, wadanda aka bayar da sunayen nasu sune kamar haka: Isa Tilde Abdullahi Mohamm...
Ban damu da zagin da ake min ba, gyaran Najeriya ne a gabana>>Shugaba Tinubu

Ban damu da zagin da ake min ba, gyaran Najeriya ne a gabana>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa yana sane da irin maganganun da ake fadi akansa amma duk basu dameshi ba saboda gyaran Najeriya ne a gabansa. Ya bayyana hakane yayin ganawa da dattawan yankin Inyamurai na kudu maso gabas a ziyarar aiki da ya kai yankin ranar Asabar. Shugaban yace yasan irin aikin da ya nema kuma yasan za'ayi ta zaginda da maganganu marasa dadi, yace amma ya toshe kunnensa. Shugaban yace cire tallafin ma da yayi duk da akwai zafi amma ya zama dole dan a samu kudin gyara kasa, musamman dan manyan gobe su ji dadi.
Gwamnatin tarayya ta ware Naira Biliyan 100 dan ciyar da yara ‘yan Makaranta a shekarar 2025

Gwamnatin tarayya ta ware Naira Biliyan 100 dan ciyar da yara ‘yan Makaranta a shekarar 2025

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya a cikin kasafin kudin shekarar 2025 ta ware Naira Biliyan 100 dan ciyar da yara 'yan Makarantar Firamare. Tsarin ciyarwar an fito dashi ne dan kawar da matsalar rashin samun abinci me gina jiki da yaran ke fama da ita da kuma karfafa ilimi da karfafa gwiwar manoma. A kokarin inganta tsarin, Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, zata yi kokarin ganin an magance matsalolin shirin kama daga rashin biyan masu aikin da manoma da rashin baiwa daliban abinci me kyau.
Jamb ta samu kudin shiga Biliyan 22.9 inda ta baiwa gwanatin tarayya Naira Biliyan 6

Jamb ta samu kudin shiga Biliyan 22.9 inda ta baiwa gwanatin tarayya Naira Biliyan 6

Duk Labarai
Hukumar shirya jarabawar shiga jami'a ta Jamb ta sanar da cewa ta baiwa gwamnatin tarayya kudi shiga da suka kai Naira Biliyan 6 a shekarar 2024. Kakakin JAMB, Dr Fabian Benjamin ne ya bayyana haka a sanarwar da ya fitar ranar Litinin inda yace sun samu jimullar kudin shiga da suka kai Naira N22,996,653,265.25 a shekarar 2024 din. Yace sun baiwa Gwamnatin tarayya Naira N6,034,605,510.69 daga cikin kudin. Sanarwar tace kudin da suka baiwa gwamnatin tarayya rara ce da suka samu bayan kammala aikin shirya jarabawar ta shekarar 2024 da cire duk wasu kudade da suka kamata. Ya kara da cewa a cikin shekaru 7 da suka gabata, sun baiwa Gwamnatin tarayya jimullar kudaden shiga da suka kai naira Biliyan 50.