Najeriya ta ware biliyan 60 na ciyar da ƴan firamare a 2025
Gwamnatin Najeriya ta ware naira biliyan 60 domin ciyar da 'yan makarantar firamare a sassa daban-daban na kasar a cikin kasafin kudin 2025.
Za ai aikin ne karkashin shirin gwamnati na farfado da tattalin arziki wato Economic Recovery Growth Plan (ERGP).
Jaraidar Dailty Trust ta tawaito cewa, kafin a sauya ministan ilimin kasar ya fara sanar da hakan wanda dama shirin ciyar da daliban yake karkashin ma'aikatarsa, kafin daga bisani a mayar da shi karkashin ofishin shugaban kasa.
An ware wa ma'aikatar ilimi kudi naira biliyan 348, cikin sama da naira tiriliyan 2. 517, wanda hakan na daga cikin fannin da ya fi samun kaso mai tsoka a kasafin kudin, duk da bai kai adadin da Bankin Duniya ya bayar da shawara na kashi 20 zuwa 30 cikin 100 na kasafin kudin ba.
Har wa yau, ma'aikatar il...








