Bidiyon ministar mata da yara da tallafi ta kasar Fiji, MP Lynda Tabuya ya fita inda aka ganta tsirara haihuwar uwarta.
Ministar tace wannan bidiyo ta yi shi ne ta aikawa mijinta amma bata da masaniyar yanda aka yi ya watsu a kafafen sada zumunta.
Tuni dai Firaiministan kasar, Sitiveni Rabuka ya sauke ta daga mukaminta dalilin wannan badakala.
Saiai tace ita bata aikata laifin komai ba dan kuwa mijinta ta aikawa bidiyon amma bata san yanda aka yi bidiyon ya watsu a kafafen sada zumunta ba.
Ta gargadi masu watsa bidiyon da su yi hankali dan tasa a yi bincike dan gano wanda suka watsa shi kuma zata dauki hukuncin shari'a akansu.
Mataimakin Kwamishinan 'yansandan kasar, Livai Driu ya bayyana cewa, suna kan binciken lamarin bayan korafin da Ministar ta kai musu.
Bidiyon yanda wani Kwarto ya makale a jikin matar aure yayin da yake lalata da ita ya dauki hankula.
https://twitter.com/miondokoo/status/1872319619526266998?t=7P2vZfh9u8AYumHyTAXZgA&s=19
Lamarin yasa sai da mutane suka kai musu dauki.
Rahotanni dai sunce mijin matar ne yayi amfani da wani sihiri da ya sa hakan faruwa.
Babban maganin daina Luwadi shine tsoron Allah.
Alhamdulillahi tunda har Allah ya karkato da zuciyarka kake neman Maganin dena luwadi, wannan babban matakin hanyar shiriyane ka dauka wanda kuma idan Allah ya yarda Allah zai taimakeka akai.
Babban Abin yi yanzu shine ka yi tuba na gaskiya da nadama ta gaske akan cewa, ba zaka sake komawa ga wannan bakar dabi'ar ba sannan ka yi addu'a sosai ta neman gafarar Allah domin Allah yana gafarta kowane zunubi matukar ba shirka bane aka mutu ana yi.
Sannan ka roki Allah ya taimakeka wajan kokarin daina wannan dabi'ar.
Hanyoyin Daina Luwadi
Allah madaukakin sarki yana cewa, "Kace yaku bayina da kuka zalunci kawunanku(ta hanyar aikata zunubai, kada ku yanke tsammani daga rahamar Allah, lallai Allah yana gafarta duka zunubai, Lallai shin...
Babban maganin daina sata shine tsoron Allah.
Sata indai ba ta cuta bace wadda ita kuma matsayinta daban, mutum zai sawa ransa kudirin dainawa ne, da kuma tuba da mayar da abinda ya sata da yin nadama akan abinda ya aikata. Idan kuma mutum bai da halin mayar da abinda ya sata ga maishi, watau ko ya kare kuma baida dukiyar da zai mayar da madadinsa, kuma bai da karfin da zai je ya nema, watau yayi aiki ya samu kudi ya biya, to sai ya tuba ga Allah.
Akwai sata ta cuta wadda a likitance ake kiranta da sunan Kleptomania.
Ita wannan sata ta cuta tana da alaka da rashin lafiyar kwakwalwa, wanda suke da ita mafi yawanci masu hali ne kuma basu da yawa a Duniya, kuma sukan saci abinda sun ma fi karfinshi ko kuma babu abinda zai amfanesu dashi.
Hakanan masana sunce ita irin wannan cutar...
Rahotanni daga kasar Pakistan na cewa, kasar Afghanistan ta kai mata hari da jiragen yaki na sama wanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutane akalla 46.
Wadanda suka mutun wanda yawanci matane da kananan yara kamar yanda gwamnatin kasar ta Afghanistan ta tabbatar.
Hakanan akwai karin mutane 6 da suka mutu sanadiyyar karin wasu hare-haren da kasar ta Pakistan ta kai a kasar ta Afghanistan.
Ma'aikatar harkokin kasashen waje ta Afghanistan tuni ta kira wakilin jakadan Pakistan dake kasarta inda ta yi Allah wadai da lamarin tare da shan Alwashin kai harin ramuwar gayya.
Kafar Reuters tace kasar Pakistan ta kaiwa 'yan Bindigar TTP harine biyo bayan harin da suka kai a kudancin Waziristan daya kashe sojojin Pakistan din guda 16.
TTP ta hada kai da Kungiyar Taliban amma tana kai harin...
Tauraron kwallon kafar kasar Misra, Muhammad Salah ya saka hotunan kwalliyar Kirsimeti da yayi da iyalansa a shafukansa na sada zumunta.
Lamarin dai ya jawo cece-kuce kamar ko da yaushe inda wasu da yawa suka sokeshi
A dazu ne muka samu labarin yanda sojojin Najaria suka gamu da harin Kungiyar B0k0 Hàràm wanda ta kai musu da jirgi marar matuki.
Wadannan hotunan jirgin da aka kai harin dashine.
Harin dai ya lalata motar sojoji daya.
A yayin da ya rage saura kwanaki kadan mu shiga shekarar 2024, mun kawo muku jadawalin alkawuran da Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta yi wadanda bata cikasu ba a wannan shekarar.
Alkawarin cire haraji akan kayan Abinci
Cire Haraji akan kayan Abinci dan samarwa talakawa hanyar saukin rayuwa abune da gwamatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta alkawarta ta bakin Ministan Noma, Abubakar Kyari.
Yace za'a cire haraji akan Alkama, Shinkafa, Masara da sauransu dan samarwa mutane saukin rayuwa.
A ranar 14 ga watan Augusta, Hukumar Kwastam ta sanar da izinin data samu daga fadar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu dan cire tallafin.
Hukumar kwastam tace cire harajin zai fara aiki ne daga 15 ga watan July zuwa 15 ga watan Disamba.
Saidai da ba'a ga an cire harajin ba, an ...