Saturday, March 14
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Rundunar ‘yansanda a Katsina ta ce ta kashe ‘yanfashi 40 a 2024

Rundunar ‘yansanda a Katsina ta ce ta kashe ‘yanfashi 40 a 2024

Duk Labarai
Kwamashinan 'yansanda na jihar Katsina da ke arewacin Najeriya, Aliyu Musa, ya ce rundunarsu ta kashe 'yanfashin daji 40 daga farko zuwa ƙarshen shekarar 2024. Da yake magana yayin wani taron manema labarai na ƙarshen shekara a birnin Katsina ranar Litinin, kwamashinan ya ce sun kuma ceto mutanen da aka yi garkuwa da su 319, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito. Kazalika a cewarsa, sun kama aƙalla mutum 916 a wannan tsakanin. "Mun samu nasarar ɗaiɗaita gungun miyagu da dama, mun ƙwato makamai, mun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su, sannan mun yi nasarar gurfanar da wasu da dama a gaban kotu," in ji shi.
Akwai yiwuwar Man United ta koma ƙasan teburi – Amorim

Akwai yiwuwar Man United ta koma ƙasan teburi – Amorim

Duk Labarai
Shekara 50 kenan rabon da Manchester United ta faɗi daga gasar Premier League. Man United na ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da suka zarta kowacce samun nasara a Ingila da ma duniya baki ɗaya, kuma mun saba ganin kulob ɗin yana shiga tsaka mai wuya a lokuta daban-daban. Sai dai a wannan karon lamarin ya sha bamban. A daren da ya gabata ne Newcastle ta doke Man United 2-0 har gida. Bayan kammala wasan da Newcastle ɗin ta ɗaiɗaita United a minti 30 na farko, mai horarwa Ruben Amorim ya fara tunanin faɗawa "relegation zone" - wato komawa ƙasan teburi. Da sashen BBC Sport ya tambaye shi game da ko suna ƙoƙarin guje wa faɗawa ƙasan teburin a yanzu, Amorim ya amsa da cewa: "ina akwai yiwuwar hakan. Dole ne mu faɗa wa magoya bayanmu gaskiya." Sakamakon wasan ya sa United ta koma ta 14 a...
Hisbah ta fara kwashe yaran da ke gararamba kan titunan Kano

Hisbah ta fara kwashe yaran da ke gararamba kan titunan Kano

Duk Labarai
Gwamnatin Kano ta fara kwashe 'dubban' yara da ke rayuwa a kasuwanni da ƙasan gadoji a Kano, babban birnin jihar. Gwamnatin ta fara ɗaukar matakin ne a jiya Litinin, inda ta samar da wani sansanin ajiyewa da kuma tantance yaran. Shugaban hukumar Hisbah a jihar, Sheikh Aminu Daurawa ya ce "mun samu rahoton akwai ɗaruruwa ko kuma dubban ƙananan yara da ba su haura shekara 15 ba waɗanda suke kwana a ƙarƙashin gadoji da cikin tashoshi da kuma kasuwanni." "Ci gaba da rayuwarsa a waɗannan wurare zai iya haifar da matsala ta tsaro da ta zamantakewa a nan gaba," in ji Daurawa. Shugaban na hukumar Hizba ya ce alƙaluman da suke da su sun nuna cewa akwai irin waɗannan yara masu gararamba a kan tituna sama da 5000. Ya kuma bayyana cewa za a tara yaran da aka kwashe ne a wata cibiya, ind...
Tinubu na cikin mutanen da suka fi tsara manyan laifuka da rashawa a 2024 – OCCRP

Tinubu na cikin mutanen da suka fi tsara manyan laifuka da rashawa a 2024 – OCCRP

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu na cikin na gaba-gaba a jerinn mutanen da suka fi tsara manyan laifuka da kuma aikata cin hanci da rashawa, a cewar rahoton cibiyar kula da aikata manyan laifuka da rashawa ta duniya. CIbiyar Organized Crime and Corruption Reporting Project (OCCRP) kan nemi 'yanjarida da ƙwararru da ɗaiɗaikun mutane su kaɗa ƙuri'a wajen zaɓen mutanen da suka fi aikata tsararrun laifkuka a ɓangaren cin hanci da rashawa duk shekara. Tinubu ne ya zo na uku a jerin, yayin da tsohon Shugaban Syria Bashar al-Assad ya zo na ɗaya "saboda abubuwan da suka faru a ƙasar a baya-bayan nan," in ji OCCRP. Sai dai zuwa yanzu gwamnatin Najeriya ko Tinubu kansa ba su ce komai ba game da sakamakon ƙuri'ar. Duk da cewa shi ne ya fi kowa yawan ƙuri'u, Shugaban Kenya William Ruto n...
Ka daina karya saboda ka kai shekaru 80>>Kwankwaso ya gayawa Atiku

Ka daina karya saboda ka kai shekaru 80>>Kwankwaso ya gayawa Atiku

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana cewa, bai kamata mutane da suka kai shekaru 70 zuwa 80 ba su rika karya. Ya bayyana hakane a matsayin martani ga maganar Atiku Abubakar ta cewa sun hada kai dan kwace mulki daga hannun APC a shekarar 2027. Kwankwaso ya bayyana cewa wannan magana bai san da ita ba kuma jinta ya bata masa rai. Yace wannan ne matsalar Najeriya. ya kara da cewa, Jam'iyyar PDP ta mutu ne shiyasa take nema sai ta hada kai da wasu jam'iyyun kamin ta samu nasarar karbar Mulki.