Friday, April 24
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Matatar Man Fetur din Dangote ta dakushewa fetur din kasashen Turai kasuwa

Matatar Man Fetur din Dangote ta dakushewa fetur din kasashen Turai kasuwa

Duk Labarai
Kungiyar kasashe masu arzikin man fetur, OPEC ta bayyana cewa, matatar man fetur ta Dangote tasa farashin man fetur ya karye a kasuwar kasashen Turai. Rahoton yace, Matatar man ta Dangote ta fitar da Man fetur, da man jirgin sama da Gas da sauransu. Rahoton ya kara da cewa, a baya Najeriya ta dogara ne kacokan wajan shigo da man fetur daga kasashen waje amma yanzu lamarin ya canja. Hakanan matatar man ta Dangote ba kasashen Africa kadai take sayarwa da Man fetur din ba, hadda kasashen Asia da sauransu. Ana sa ran a yayin da karfin mamatar da yawan kasashen da take fitarwa da man fetur ke karuwa, zata ci gaba da dakushewa kasuwar man fetur ta kasashen Turai Armashi.
Wani Mutum ya rasu a Abuja a hotel lokacin da suke tare da budurwarsa data taso tun daga jihar Jigawa ta kai masa ziyara

Wani Mutum ya rasu a Abuja a hotel lokacin da suke tare da budurwarsa data taso tun daga jihar Jigawa ta kai masa ziyara

Duk Labarai
Innalillahi Wa Inna Ilaihir Rajiun Wani Mutum ya rasu yau a Abuja a hotel lokacin da suke aikata zina shida budurwar sa da suka hadu a social media Bincike ya tabbatar da cewa Ƙwayoyin kara karfin maza ne yayi sanadiyar mutuwar tasa, ita budurwar tasa ƴar jahar Jigawa ce Ƙaramar Hukumar Dutse, tayi karya taje har Abuja ta same shi Allah ya tsare mu da mummunar kaddara. Cikakken Bayani: MARYAM TA JE ABUJA KARBAN iPhone 16 KO? LISSAFI YA KWABE!, DARASIN RAYUWA! Dazu da safe, Manajan gidan hotel na Palasa dake yankin Gwagwalada Abuja ya kai kara ofishin 'yan sanda na Gwagwalada bayan wani mutum ya mutu a dakin hotel din da ya kama shi da wata karuwa Sunan wanda ya mutu Lawal Ibrahim, sunan karuwarsa kuma Maryam Abba daga birnin Dutsen Jihar Jigawa, wanda sun hadu a social...
DSS ta sake kama dan Gwagwarmaya Mahadi Shehu

DSS ta sake kama dan Gwagwarmaya Mahadi Shehu

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan farin kaya ta DSS ta sake kama dan Gwagwarmaya Mahadi Shehu a Kaduna. Rahoton Daily Trust yace an kama Mahadi Shehu ne a Unguwar Dosa da misalin karfe 11 na safe. Saidai zuwa yanzu babu karin bayanin dalilin kamashi. A watan Disambar da ya gabata ne dai aka kama Mahdi Shehu bisa zargin watsa labarin da ba daidai ba. Na kusa dashi sun bayyana cewa suma basu san dalilin kamen ba.
Gwamnan Jihar Naija ya bada shawarar a rika amfani da yaren Hausa wajan koyar da yara a makarantun Firamare da Sakandare a jihohin Arewa

Gwamnan Jihar Naija ya bada shawarar a rika amfani da yaren Hausa wajan koyar da yara a makarantun Firamare da Sakandare a jihohin Arewa

Duk Labarai
Gwamnan jihar Naija, Muhammad Bago ya bayar da shawarar a rika amfani da yaren Hausa wajan koyar da dalibai a makarantun Firamare da Sakandare a jihohin Arewacin Najeriya. Ya bayyana hakane a wajan wani taro da aka yi a Minna ranar Talata inda yace daukar wannan mataki zai kara karfafawa yara shiga makaranta. Yace kamata yayi a rika Amfani da Turanci a matsayin Subject kawai amma ba yaren koyar da karatun ba. Gwamnan ya jawo hankalin Gwamnonin Arewa dasu canja tsarin karatun yankin dan karfafa gwiwar yara su shiga makaranta.
Facebook zai kori ma’aikata dubu uku

Facebook zai kori ma’aikata dubu uku

Duk Labarai
Kamfanin Meta dake da mallakar manhajojin Facebook, Thread, Instagram da WhatsApp na shirin korar ma'aikata 3600 daga aiki Za'a kori ma'aikatan aiki ne saboda rashin kwazo inda za'a maye gurbinsu da wasu kamar yanda kafar Bloomberg ta ruwaito. Wadannan ma'aikatan na wakiltar kaso 5 na kafatanin ma'aikatan kamfanin na Meta. Kamfanin dai na da jimullar ma'aikata 72,400. Shugaban kamfanin, Mark Zuckerberg ya bayyana cewa ya yanke shawarar mayar da hankali kan kwazon ma'aikata.
Babban Bankin Najeriya ya ci bankunan UBA, First Bank, Zenith Bank, Fidelity tarar Naira Miliyan dari da hamsin kowannensu saboda kin sakawa kwastomominsu kudi a ATM

Babban Bankin Najeriya ya ci bankunan UBA, First Bank, Zenith Bank, Fidelity tarar Naira Miliyan dari da hamsin kowannensu saboda kin sakawa kwastomominsu kudi a ATM

Duk Labarai
Babban bankin Najeriya, CBN ya ci tarar bankuna da yawa saboda kin sakawa kwastomominsu kudi a ATM su cire musamman lokacin bukukuwan karshen shekara. Bankin yace ya dauki wannan mataki ne dan nuna rashin amincewa da kin rabawa mutane kudi da bankunan ke yi. CBN yaci kowane bankin tarar Naira Miliyan 150. Hakan ya biyo bayan gargadin da bankin yawa bankunan na su wadata mutane da kudi amma suka ki yi, CBN ya aika wakilai zuwa wadannan bankunan kamin daukar matakin tarar. Bankunan da aka ci tarar sune, Fidelity Bank Plc, First Bank Plc, Keystone Bank Plc, Union Bank Plc, Globus Bank Plc, Providus Bank Plc, Zenith Bank Plc, United Bank for Africa Plc, da Sterling Bank Plc.
Abin da ya sa na fice daga jam’iyyar PDP – Bafarawa

Abin da ya sa na fice daga jam’iyyar PDP – Bafarawa

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Sokoto a Najeriya, Dalhatu Attahiru Bafarawa, ya sanar da ficewar shi daga babbar jam'iyyar adawa ta ƙasar - PDP. Bafarawa ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ta ɓulla a yau Talata 14 ga watan Janairun 2025, wadda ya sanya wa hannu da kansa. A cikin wasiƙar ficewa daga jam'iyyar, wadda ya rubuta wa shugaban jam'iyyar na ƙasa a ranar 8 ga watan Janairu, Bafarawa ya ce: "Na rubuto wannan takarda domin gabatar da matakin ficewa daga jam'iyyar PDP". Ya ƙara da cewa "duk da cewa wannan mataki, wanda na ƙashin kaina ne kuma ba mai sauƙi ba, na ɗauke shi ne sanadiyyar mayar da hankalin da na yi kan wani sabon babi na aiki na daban, wanda ya yi daidai da manufata ta bunƙasa al'umma ta hanyar ƙarfafa matasa." Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da jam'iyyar ta P...
Farashin litar mai a Najeriya zai sake haura naira dubu daya

Farashin litar mai a Najeriya zai sake haura naira dubu daya

Duk Labarai
Kungiyar dillalan man fetur ta Najeriya wato IPMAN, ta ce farashin litar man fetur a gidajen mai zai zarta naira dubu daya nan da kwanaki masu zuwa. IPMAN ta ce karin ya zama dole sakamako karin farashin da hukumar fiton man fetur da sanya ido kan sayar dashi ta NMDPRA ta yi. Alhaji Salisu Ten Ten, shugaban kungiyar dillalan man fetur ta Arewacin Najeriya wato IPMAN, ya shaida wa BBC cewa, a shekarun baya man fetur daga kasashen waje ake shigo dashi, sai gashi kuma bayan matatar man fetur ta Dangote ta fara aiki sai aka daina shigo da man. Ya ce, " A lokacin da ake shigo da mai daga kasashen waje akwai harajin naira 10 kan kowacce lita da duk wanda ya shigo da mai yake biyan hukumar NMDPRA, to a yanzu saboda an daina shigo da man sakamakon matatar mai ta Dangote sai dillan man suk...
Idan ku ka amince a ƙaro mana tankar yaƙi 50 to a wata biyu za mu gama da ƴan ta’adda – Ministan tsaro

Idan ku ka amince a ƙaro mana tankar yaƙi 50 to a wata biyu za mu gama da ƴan ta’adda – Ministan tsaro

Duk Labarai
Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, ya nemi Majalisar Wakilai ta saka kuɗaɗen karin tamkar yaƙi guda 50 a kasafin kudin 2025 don magance matsalar ƴan ta'adda a kasar. Badaru Abubakar ya yi wannan roƙon ne a yau Talata yayin zaman kare kasafin kudin 2025 da kwamitin tsaro na majalisar ya shirya a Abuja. Ya bayyana cewa, tare da wannan kayan aiki, za a kawo karshen matsalar ƴan ta'adda a cikin watanni biyu. “Ma’aikatar Tsaro na da alhakin samar da wasu kayan aiki a wasu yankuna, amma ba mu da damar yin hakan. “Daga abin da mu ka samu a 2024, mun iya samar da Motoci Masu Sulke guda 20 kawai, amma me za su iya yi? “Idan mu ka samu karin motocin guda 50 da za su shiga dazuzzuka don fatattakar ‘yan ta’adda, ina tabbatar muku, cikin wata biyu za mu kawo karshen matsalar 'yan ...
Hukumar Customs ta samarwa da Gwamnati kudin shiga Naira Tiriliyan 6.105 a shekarar 2024

Hukumar Customs ta samarwa da Gwamnati kudin shiga Naira Tiriliyan 6.105 a shekarar 2024

Duk Labarai
Hukumar Kwastam ta samarwa da gwamnatin tarayya kudin shiga sa suka kai Naira Tiriliyan 6.105 a shekarar 2024. Shugaban hukumar, Mr Adewale Adeniyi ne ya bayyana haka a yayin da yake gayawa manema labarai yanda hukumar ta gudanar da ayyukanta a shekarar 2024. Yace kudin shigar da suka samarwa gwamnatin ya zarta kudin da gwamnatin ta bukaci su samar mata na Tiriliyan 5.079