Friday, February 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Matawalle na da hannu a aikin ƴan fashin jeji, in ji Gwamnan Zamfara

Matawalle na da hannu a aikin ƴan fashin jeji, in ji Gwamnan Zamfara

Siyasa
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi zargin cewa magabacinsa, Bello Matawalle, na da hannu dumu-dumu a aiyukan ƴan fashin jeji da suka addabi jihar. Jaridar PUNCH ta rawaito cewa da ya ke magana a wani shirin siyasa na gidan talabijin na TVC a daren jiya Laraba, gwamnan ya yi ikirarin cewa, bisa bayanan da su ka samu, magabacinsa ya jagoranci gwamnatin da ke hada kai da ƴan fashin jeji su na aikata ta'addanci. Lawal ya kuma zargi gwamnatin da ta shude a karkashin Bello Matawalle, wanda a yanzu shi ne karamin ministan tsaro da karkatar da kudaden jihar da kuma yin sakaci da harkar tsaro a jihar. “Eh, akwai batutuwa da yawa a baya daga gwamnatin da ta gabata. A gaskiya, bari in fadi wannan sarai: da nine shi (Matawalle) zan yi murabus in fuskanci duk wani zargi da ake min, haka...
Sheikh Nura Khalid Ya Halarci Taron Mabiya Shi’a Mai Taken ‘Makon Hadin Kai’

Sheikh Nura Khalid Ya Halarci Taron Mabiya Shi’a Mai Taken ‘Makon Hadin Kai’

Duk Labarai
Taro ne dai wanda shugaban mabiya Shi'a na Nijeriya Sheikh Ibrahim Zakzaky ke jagoranta, an gudanar da shine a jiya Laraba a Abuja, inda ake gudnarwa domin haɗa kan malamai daga ɓangarori daban-daban dake fadin kasa baki daya, kama daga musilmai da Kìrìstòcì, inda kowane banhare ke amsa gayyata tare da yin jawabai da suke da alaƙa da haɗin kai da zaman lafiya. An gabatar da taron ne a Abuja inda malamin ya yi Magana akan Soyayyar Manzon Alĺàh SAW tare da amfanin hadin kai. Me za ku ce? Daga Abba Abdulaziz Fari Funtua
Matar Shugaba Tinubu Ta Bada Gudummuwar Naira Milyan 500 Ga Al’ummar Maiduguri

Matar Shugaba Tinubu Ta Bada Gudummuwar Naira Milyan 500 Ga Al’ummar Maiduguri

labaran tinubu ayau, Siyasa
Uwargidan shugaban Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta bayar da gudunmuwar Naira miliyan 500 ga gwamnatin jihar Borno ta hanyar shirinta na Renewed Hope Initiative domin tallafawa wadanda bala'in ambaliyar ruwa ya rutsa da su a Maiduguri. Uwargidan mataimakin shugaban kasa Hajiya Nana Shettima ta wakilci uwargidan mataimakin shugaban kasa kuma mataimakiyar shugaban kungiyar Renewed Hope Initiative, Uwargidan shugaban kasar ta jajantawa al'ummar Borno bisa bala'in da ya yi sanadiyar salwantar rayuka da dukiyoyi da rayuwa ¹. A yayin bayar da gudummawar a gidan gwamnati, Hajiya Nana Shettima ta yaba wa Gwamna Farfesa Babagana Umara Zullum bisa gaggauwa da gaggawar da ya dauka kan bala’in da kuma tallafin da aka ba wa wadanda abin ya shafa. Gwamnan ya nuna godiya ga Sanata Oluremi Tinubu bi...
Kwankwaso Ya Bada Gudunmawar Naira Milyan Hamsin Ga Waɗanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Jihar Borno

Kwankwaso Ya Bada Gudunmawar Naira Milyan Hamsin Ga Waɗanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Jihar Borno

Rabiu Musa Kwankwaso
Daga Abubakar Shehu Dokoki Ɗan Takarar Shugaban ƙasa, ƙarkashin Tutar Jam'iyyar NNPP a zaɓen daya gabata na 2023 Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bada wannan tallafin ne a wata ziyara ta musamman da ya kai jihar Borno domin jajanta musu bisa ambaliyar ruwan da ta yi sanadiyyar raba ɗaruruwan mutane da gidajensu. Kwankwaso ya miƙa wannan tallafi ne ta hannun Gwamnatin Jihar Borno.
Ganin Bidiyon babiana tsirara ya jawo cece-kuce a Tiktok, Kalli Bidiyon martaninta

Ganin Bidiyon babiana tsirara ya jawo cece-kuce a Tiktok, Kalli Bidiyon martaninta

Babiana
Fitowar Bidiyon Tauraruwar Tiktok Babiana tsirara ya jawo cece-kuce a kafar Babiana dai ta yi suna sosai wajan kawo labarai akan abubuwan dake faruwa na yau da kullun musamman akan wanda mutane basa kyautawa. A wannan karin sai ga Bidiyonta ya fito tsirara wanda da yawa suka bayyana da cin zarafi a garet. Wasu sun yabama karfin gwiwarta inda wasu suka bata shawarar ta kai maganar kotu. Bidiyo ya bayyana na Babiana inda ta yi martani kan wannan Bidiyo nata da ya fita. https://twitter.com/arewablog_/status/1836500067991117929?t=iOz1mbCCglYjQ83JPVXb9g&s=19 Da alama dai Babiana ta nuna ko a jikinta.
Rikicin Aminu J Twon, Ordinary President da matar soja, Waye me gaskiya?

Rikicin Aminu J Twon, Ordinary President da matar soja, Waye me gaskiya?

Duk Labarai
Matar soja Seaman Haruna Abbas ta dauki zafi sosai akan neman taimakon da Aminu J. Town yace ya mata inda ta yi ikirarin cewa ba da saninta bane. Hakanan Shima Ordinary President, Ahmad Isah wanda ta je gidan talabijin da rediyonsa wajan neman hakkin mijinta, ya dauki zafi duk da dai yawa Aminu J. Town Nasiha. Hakanan a bangaren Aminu J. Town, shima bai dauki abin da sauki ba inda yayi zargin cewa ana son bata masa suna. Aminu J. Town dai ya bayyana cewa an nemi ya tarawa matar sojan ruwa, Seaman Haruna Abbas wadda ta kai kara gidan talabijin na Ordinary president inda tace an tsareshi tsawon shekaru 6 ba tare da hukunci ba kan zargin yayi yunkurin kashe ogansa. J Town yace yayi kokarin neman lambar matar inda ya kira dan neman izinin tara mata taimakon. Ga bidiyon wayar da ...
Wahala ta yi yawa, A tausayawa Talakawa>>Tsohon Shugaban kasa,Abdulsalam Abubakar ya roki Gwammati

Wahala ta yi yawa, A tausayawa Talakawa>>Tsohon Shugaban kasa,Abdulsalam Abubakar ya roki Gwammati

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa,Abdulsalam Abubakar ya gayawa Gwamnati cewa wahalar da ake ciki a kasarnan ta yi yawa. Ya bayyanawa manema labarai cewa,mutane da yawa a yanzu basu da kudi inda kudin mota da sauran ababen hawa suka karu ga kudin makarantar yara ya karu kuma mutane basa iya cin abinci sau 3 a rana. Yace shi da wasu masu fada a ji sun baiwa gwamnatin tarayya shawarar yanda za'a fita daga cikin halin da ake ciki. Daya daga cikin hanyoyin kamar yanda yace sune gwamnatin ta sayi abinci ta rika sayarwa a farashi me sauki. Ya kuma bayar da shawara ga masu shirin yin zanga-zangar tsadar rayuwa ta ranar 1 ga wata October da kada a tayar da hankali a yi ta cikin lumana.
Najeriya Za ta Zama Jagorar Kasuwar Halal Ta Duniya Mai Jarin Dala Bilyan Dubu 7- Kashim Shettima

Najeriya Za ta Zama Jagorar Kasuwar Halal Ta Duniya Mai Jarin Dala Bilyan Dubu 7- Kashim Shettima

Duk Labarai
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bayyana cewa Najeriya na kan gaba a fannin tattalin arziki ta bangaren Kasuwar Musulmi zalla da ake kira da Kasuwar halal ta duniya, wadda aka yi hasashen jarinta zai haura Dalar Amurka tiriliyan 7.7 a shekarar 2025. Kashim ya bayyana haka ne a wajen taron masu ruwa da tsaki na tattalin arzikin Halal da aka gudanar a dakin taro na Banquet Hall dake fadar shugaban kasa a Abuja a yau Laraba, 18/09/24. Mataimakin ya jaddada cewa girman tattalin arzikin Najeriya da yawan al'ummarta yana samar mata da damammaki musamman a bangaren bunkasa sashen saka hannun jari na halal. Kasuwar Rumbun Halal wani shiri ne da ya kunshi sayar da ababen da addinin Musulunci ya halasta da suka hada da halatattun abinci da abin sha, da kayan kwalliya, da na gyara...