Friday, February 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

ALLAHU AKBAR: An Yi Jana’izar Mutane 41 Da Sùķa Ŕaśù Sakamakon Hàďaŕìn Moțà A Hanyar Su Ta Zuwa Wajen Zagayen Mauĺùďì Daga Garin Kwandari Zuwa Samunaka

ALLAHU AKBAR: An Yi Jana’izar Mutane 41 Da Sùķa Ŕaśù Sakamakon Hàďaŕìn Moțà A Hanyar Su Ta Zuwa Wajen Zagayen Mauĺùďì Daga Garin Kwandari Zuwa Samunaka

Duk Labarai
An Yi Jana'izar Mutane 41 Da Sùķa Ŕaśù Sakamakon Hàďaŕìn Moțà A Hanyar Su Ta Zuwa Wajen Zagayen Mauĺùďì Daga Garin Kwandari Zuwa Samunaka Mahalarta mauludin sun yi gamu da ajalin na su ne a jiya Lahadi, a loķacin da motar su ta yi arañģàmà da tireĺa a daidai garin Lere, inda kimanin mutane talatìn sùka mùțù nañ take, yayin da kaŕin mutane sha daya suka ŕaśu bayan an kai su asibiti domin jinyar su sakamakon raunin da suka samu. Allah Ya gafarta musu. Daga Umar Isa Ramin Kura
Kwamitin kula da sha’anin sojojin ruwa (Navy) na majalisar dokoki ta tarayya sun gana da hukumar Sojin ruwa domin binciko zargin yadda aka ci zarafin Seaman Abbas Haruna

Kwamitin kula da sha’anin sojojin ruwa (Navy) na majalisar dokoki ta tarayya sun gana da hukumar Sojin ruwa domin binciko zargin yadda aka ci zarafin Seaman Abbas Haruna

Duk Labarai
Kwamitin kula da sha'anin sojojin ruwa (Navy) na majalisar dokoki ta tarayya sun gana da hukumar Sojin ruwa domin binciko zargin yadda aka ci zarafin Seaman Abbas Haruna tsawon shekara 6 bisa umurnin wani babban jami’in Jeneral MS Adamu. Majalisar ta lashi takobin yin binciken ƙwakwaf akai domin hukunta duk wanda aka samu da laifi a lamarin Wane fata zaku yi musu ?
‘Muna fargabar barkewar cutuka masu muni a Maiduguri’

‘Muna fargabar barkewar cutuka masu muni a Maiduguri’

Duk Labarai
Masana harkokin lafiya a Najeriya sun yi kira ga gwamnatin kasar da ta aike da tawagar likitoci na musmaman da suka kware kan cututuka masu yaɗuwa zuwa Borno saboda fargabar barkewar cututuka sakamakon ambaliyar ruwan da aka fuskanta a jihar. Masanan sun ce, suna fargabar barkewar cututuka irinsu zazzabin cizon sauro, da Zika, da zazzabin typoid, da na dange, da kuma uwa uba amai da gudawa, sakamakon irin dattin da ambaliyar ruwa ta kwaso da gawarwakin makabartu da ruwan ya dauko. Dr Nasiru Sani Gwarzo, babban sakataren ma'aikatar Ilimi a Najeriya, kuma masani kan harkokin kiwon lafiya ya shaida wa BBC cewa, dole ne hukumomi su gaggauta shawo kan ruwan da ya malale asibitin koyarwa na Maiduguri saboda wasu daga cikin na'urorin asibitin akwai wadan ke da sinadarin nukiliya a ciki da k...
Dangote ya karyata maganar NNPCL cewa a farashin Naira 898 ya sayar musu da man fetur

Dangote ya karyata maganar NNPCL cewa a farashin Naira 898 ya sayar musu da man fetur

Duk Labarai
Matatar man fetur ta Dangote ta musanta ikirarin kamfanin mai na kasa,NNPCL da yace ya sayo mai na farko daga Dangote akan farashin Naira 898 akan kowace lita. Me magana da yawun kamfanin,Mr Olufemi Soneye ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar. Yace da dala aka sayar musu da danyen man fetur dun da suka saya dan haka suma da dala suka sayarwa da kamfanin na NNPCL da tataccen man fetur din. Ya bayyana cewa kuma mansu zai isa kowane sako da lungu na kasarnan. Yace a saurari kwamitin da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya kafa kan lamarin shine zai bayyana farashin man nasu.
Obasanjo,Abdulsalam, da Ali Gusau da IBB sun yi zama na musamman kan halin da Najeriya ke ciki

Obasanjo,Abdulsalam, da Ali Gusau da IBB sun yi zama na musamman kan halin da Najeriya ke ciki

Duk Labarai
Tsaffin shuwagabannin kasa,Olusegun Obasanjo,Janar Ibrahim Badamasi Babangida, Abdulsalam Abubakar da Janar Ali Gusau sun yi zama na musamman a kan halin da Najeriya ke ciki. Sun yi zamanne a gidan tsohon shugaban kasa, IBB dake Minna. Wata majiya ta bayyana cewa, Rahotannin sun nuna an yi zamanne kan matsalar da Najeriya ke ciki musamman halin matsin tattalin arziki.

Amfanin albasa a gashi

Gyaran Gashi
Albasa na daya daga cikin abubuwan da ake amfani dasu wajan gyaran gashi da sawa yayi tsawo da kuma kara masa kwari. Yanda ake hadin shine ana samun Albasa a bare. Sai a yayyankata kanana-kanana a saka a abin markade a markada ko a daka. A tabbatar ta yi ruwa, sai a tace. Ana hada ruwan da man kwakwa a rika shafawa akai ko a hada da man shampoo da ake dashi a gida, yana taimakawa sosai wajan gyaran gashi da kara mai tsawo. Ana hada wannan ruwa na Albasa da ruwan lemun tsami musamman dan a batar da warin Albasar. Hakanan ruwan Albasan yana taimakawa wajan hana gashi fara furfura da wuri. A wani kaulin ma yana taimakawa wajan boye furfura. Ana iya hadashi ruwan lemun tsami a shafa akai na tsawon mintuna 30 sannan a wanke. Dan samun sakamako, a yi hakan sau 2 a sat...
A farashin 898 muka sayi man fetur daga matatar man Dangote>>NNPCL

A farashin 898 muka sayi man fetur daga matatar man Dangote>>NNPCL

Duk Labarai
Kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya bayyana cewa, a farashin Naira 898 suka sayi man fetur daga matatar man fetur ta Dangote. A yau ne dai kamfanin na NNPCL suka fara daukar man fetur din daga matatar man ta Dangote bayan shan dambarwa tsakanin Gwamnati da matatar man. Masu sharhi da yawa na ganin cewa, sayen man fetur din a wannan farashin daga matatar Dangote na nufin bata canja zani ba. Inda wasu ke zargin cewa, Gwamnati ce ta yi kaka gida a lamarin shiyasa man yayi tsada haka. A baya dai ana tsammanin matatar man fetur ta Dangote zata kawo saukin Man fetur a kasarnan amma hakan da kamar wuya.
Kalli Bidiyon yanda mataimakin shugaban kasa ya yanke jiki ya fadi yana tsaka da jawabi

Kalli Bidiyon yanda mataimakin shugaban kasa ya yanke jiki ya fadi yana tsaka da jawabi

Duk Labarai
Mataimakin shugaban kasar Afrika ta kudu, Paul Mashatile ya yanke jiki ya fadi yana tsaka da jawabi. Bidiyon faruwar lamarin ya yadu a kafafen sada zumunta sosai. Lamarin ya farune a garin Tzaneen dake Limpopo na kasar. https://www.youtube.com/watch?v=ueg3tH9HQPo?si=6TJ8xuSioycqCIlS Rahotanni sunce mataimakin shugaban kasar ya fadi ne saboda tsananin zafi da ake yi. Ba dai a kaishi Asibiti ba dan lamarin bai yi muni ba.