Friday, February 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Matar soja Abbas mai suna Husaina Iliyasu ta cika gwarzuwa kuma jarumar da samun irin ta sai an tara mata 1000

Matar soja Abbas mai suna Husaina Iliyasu ta cika gwarzuwa kuma jarumar da samun irin ta sai an tara mata 1000

Duk Labarai
TSANTSAR RASHIƝ IMÁNI DA TAÚSÁYI Matar soja Abbas mai suna Husaina Iliyasu ta cika gwarzuwa kuma jarumar da samun irin ta sai an tara mata 1000. Mijinta soja ne Mųsưlmi wanda daga zuwa yin Sálląh yayin da ake bakin aiki shine ogansa ya sa shi a gaba shekara da shekaru a garƙame sai da ya haukatar da shi. Tsantsar tsagwaron rashin imani ya ƙare a wannan labarin. Shin ina manyan Musulmi dake aikin soja a ƙasar nan? Shin wa ya ce a keta alfarmar ɗan adam saboda bambancin addini a aikin soja? Ina kungiyoyin kare hakkin mata? Ina kungiyar kare hakkin dan Adam? Ina kungiyar manyan Arewa? Ina kungiyar lauyoyi Musulmi? Ina kungiyar Malaman mu? Ina kungiyar yan jaridun kasar nan? Mutun ya sadaukar da rayuwar sa don ya kare ƙasa amma a ƙarshe saboda son zuciyar wani a mayar da...
Wannan an ce shine sojan da ya kashe ƙasurgumin ɗan bindigar nan Halilu Sububu, da wasu gaggan yaran ɗan bindigar

Wannan an ce shine sojan da ya kashe ƙasurgumin ɗan bindigar nan Halilu Sububu, da wasu gaggan yaran ɗan bindigar

Duk Labarai
Wannan an ce shine sojan da ya kashe ƙasurgumin ɗan bindigar nan Halilu Sububu, da wasu gaggan yaran ɗan bindigar. Waɗanda suka addabi al'ummar jihar Zamfara da sauran jihohin Arewa. An tabbatar da jarumi ne na yankan shakku, domin ance harda hannu yake kama ƴan bindiga. Allah ya ƙara kare shi a wannan aiki da yake yi. Ya kuma ƙara bashi nasara da sauran abokan aikinsa. Daga Zakari Y Adamu Kontagora
Ji Farashin da Dangote zai sayar da man fetur dinsa

Ji Farashin da Dangote zai sayar da man fetur dinsa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa farashin man fetur daga matatar man Dangote zai iya kaiwa Naira 857 zuwa 865. Kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya bayyana cewa, zai dauki man daga matatar man Dangote a farashin Naira 960 zuwa 980 akan kowace lita inda zai sayarwa da 'yan kasuwa akan farashin 850 zuwa 840. Saidai babu tabbacin ko za'a samu farashin bai daya a duka gidajen man sayar da fetur din a Najeriya. Me kula da yada labarai na kamfanin na NNPCL Olufemi Soneye ya tabbatar da cewa a ranar 15 ga watan Satumba ne zasu fara dakon man fetur din daga matatar man Dangote.

Kalli Bidiyo: Motocin dakon man fetur sun fara jigilar man daga matatar Dangote

Duk Labarai
Kamfanin matatar man fetur ta Dangote ta wallafa Bidiyon da ya nuna motocin jigilar Man fetur da suka fara jigilar man a matatar man fetur din. https://www.youtube.com/watch?v=Y9Lj_0YGDW8?si=X1CwcZDsQq5n6CW_ An fara jigilar man fetur dinne daga matatar man fetur ta Dangote bayan Dambarwar da aka sha ta cece-kuce tsakaninsa da Kamfanin mai na kasa NNPCL da kuma Gwamnatin Tarayya.
Kalli bidiyo: Yanda Wata Nurse ta yankewa likita Azzakarinsa yayin da yayi yunkurin yi mata fyade

Kalli bidiyo: Yanda Wata Nurse ta yankewa likita Azzakarinsa yayin da yayi yunkurin yi mata fyade

Duk Labarai
Wata ma'aikaciyar Jinya,Nurse dake aiki a wani Asibiti dake Bihar me suna RBS Health Care Centre ta gamu da barazanar fyade. https://www.youtube.com/watch?v=hzBaAm1qLmM?si=0YtpIarh3h_63I4R Likitan Asibitin da take aiki da wasu 3 ne suka so yi mata fyade amma basu yi nasara ba. Likitan me suna Dr Sanjay Kumar da abokan aikinsa, Sunil Kumar Gupta da Awadhesh Kumar ne suka aha giya suka yi mankas. Suka kulle kofofin shiga Asibitin inda suka afka mata. Nan dai Allah ya bata sa'a ta kama azzakarin babban likitan ta yanke da wukar fida. Ta samu ta fita da gudu kamar yanda kafar Livemint ta ruwaito. Ta samu wani waje ta labe inda ta kira 'Yansanda suka zo suka kama likitocin. Likitan dai yana can yana karbar kulawa ta musamman inda ake ci gaba da bincike.
Matar shugaban kasa,Remi Tinubu ta kashe Naira Miliyan Dari bakwai wajan yawon zuwa kasashen Duniya a cikin watanni 3 kacal

Matar shugaban kasa,Remi Tinubu ta kashe Naira Miliyan Dari bakwai wajan yawon zuwa kasashen Duniya a cikin watanni 3 kacal

Duk Labarai
Matar Shugaban kasa,Remi Tinubu ta kashe Naira Miliyan 701 a zagayen da ta yi a kasashen Duniya guda 5. Ko da a shekarar 2023 sai da fadar shugaban kasa ta warewa ofishin matar shugaban kasar Naira Biliyan 1.5 dan saya mata motoci na Alfarma. An gano hakanne a kundin tattara bayanai na gwamnatin tarayya na yanar gizo. Bayan wannan kuma, Gwamnatin ta kashewa Matar shugaban kasar Naira Miliyan 314 wajan shirya taruka a cikin gida Najeriya.
Tinubu zai dawo Najeriya bayan ziyarar da ya kai kasashen China, UAE da Ingila

Tinubu zai dawo Najeriya bayan ziyarar da ya kai kasashen China, UAE da Ingila

labaran tinubu ayau
A yau,Lahadi ne shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu zai dawo gida Najeriya bayan ziyarar da ya kai kasashen China, UAE da Ingila. Ranar 29 ga watan Augusta ne shugaban ya bar Abuja zuwa Beijing inda ya dan tsahirta a Dubai, UAE. Ya isa Beijing ranar 1 ga watan Satumba. Ranar 2 ga watan Satumba ne dai shugaban ya fara ziyarar a aikace inda ya gana da shugaban kasar China Xi Jinping sannan aka masa fareti da harbin bindiga na ban girma. A taron, Najeriya da kasar China sun sakawa wasu yarjejeniyoyi guda 5 na ci gaban kasashen biyu hannu kamar yanda kakakin shugaban kasar, Bayo Onanuga ya bayyanar. Hakanan shugaban kasar na China Xi Jinping da matarsa, Peng Liyuan sun shiryawa shugaba Tinubu wata liyafar dare wadda aka nuna al'adun kasar Chinan. Daga nan Shugaba Tinubu ya tafi z...
Kalli Bidiyon Ambaliyar ruwan Maiduguri da aka dauka daga sama

Kalli Bidiyon Ambaliyar ruwan Maiduguri da aka dauka daga sama

Duk Labarai
Ambaliyar ruwan Maiduguri na daga cikin manyan abubuwan da suka tayar da hankalin Najeriya a makon da ya gabata. Wannan Bidiyo ne na yanda ambaliyar ruwan ta kasance wanda aka dauka daga sama. https://www.youtube.com/watch?v=X2SQOOEHmQg?si=Yipd2UO4zlFedN9s https://www.youtube.com/watch?v=F-KxNLEo-kY?si=8KQKXZIlyqMI_2vL Lamarin Ambaliyar ruwan ya jefa mutane cikin halin kaka nikayi
Tsadar rayuwa tasa yanzu da yawan ‘yan Najeriya basa iya sayen magunguna>>Kungiyar masu Hada magunguna ta Najeriya

Tsadar rayuwa tasa yanzu da yawan ‘yan Najeriya basa iya sayen magunguna>>Kungiyar masu Hada magunguna ta Najeriya

Duk Labarai
Kungiyar masu hada magunguna ta koka da cewa tsadar rayuwa tasa yanzu mutane da yawa basa iya sayen magunguna. Kungiyar ta alakanta hakan da tashin farashin magunguna da kayan hadasu da karyewar farashin dala da dogaro da shigo da kayan hada magunguna da shigo da magungunan daga kasashen waje. Kungiyar ta bayyana hakane a wajan wani taro da aka yi a A Legas na masu ruwa da tsaki a cikinta.