Thursday, December 25
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Yaron Sojannan da muka lara dashi jiya sam bai da Kunya ga girman kan tsiya>>Inji Ministan Abuja, Nyesom Wike

Yaron Sojannan da muka lara dashi jiya sam bai da Kunya ga girman kan tsiya>>Inji Ministan Abuja, Nyesom Wike

Duk Labarai
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya bayyana cewa Sojan Ruwa da ya hanashi shiga wani Fili Jiya bashi da da'a sannan yana da girman kai. Ministan ya bayyana hakane ta bakin me magana da yawunsa, Lere Olayinka a yayin da ake hira dashi a gidan talabijin na Channels TV. Yace abin mamaki shine yanda ko da aka kira shugaban sojoji CDS aka baiwa sojan bai wani nuna kaduwa ba. Lamarin rikicin Wike da Sojan ne babban labarin da ake ta tattaunawa akansa a fadin Najeriya.
Da Duminsa: Naji Dadin Abinda sojan Ruwa, Yerima yawa Ministan Abuja, Wike, yayi daidai, kuma zan tabbatar babu abinda ya samu sojan>>Inji Ministan Tsaro, Muhammad Badaru

Da Duminsa: Naji Dadin Abinda sojan Ruwa, Yerima yawa Ministan Abuja, Wike, yayi daidai, kuma zan tabbatar babu abinda ya samu sojan>>Inji Ministan Tsaro, Muhammad Badaru

Duk Labarai
Ministan Tsaro, Muhammad Badaru ya bayyana goyon bayansa ga Matashin soja da ya tare Ministan Abuja, Nyesom Wike ya hanashi shiga wani fili a Abujan. Minista Badaru yace suna goyon bayan abinda Sojan yayi kuma sun jinjina masa sannan zasu bashi kariya saboda yana bakin aikinsa ne. Badaru yace zasu ci gaba da baiwa kowane soja Kariya da goyon baya muddin ya tsaya tsayin daka a bakin aikinsa. Hakan na zuwane bayan da a wajan rikicin ma sai da Wike ya kira shugaban sojoji, CDS.
Wata Sabuwa: An fara Kiraye-Kirayen a kori sojan daya tare Ministan babban birnin tarayya Abuja Nyesome Wike daga aiki

Wata Sabuwa: An fara Kiraye-Kirayen a kori sojan daya tare Ministan babban birnin tarayya Abuja Nyesome Wike daga aiki

Duk Labarai
Wasu musamman masu goyon bayan Ministan babban Birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike sun fara kiran a kori sojan ruwa da ya tare ya hana Ministan shiga wani fili a Abuja. Masu kiran dai na ganin abinda sojan yayi ya sabawa dokar kasa da kuma hana hukuma yin abinda ya dace. Sojan dai ya hana Wike Shiga wani fili ne a Abuja inda yace umarni aka bashi. Dole Wike ya fasa shiga filin inda ya tafi yana zage-zagi.
Kalli Bidiyon wasannin Barkwancin da aka fito dasu dan tsokanar Ministan Abuja, Nyesom Wike biyo bayan Tirka-Tirkar da yayi da sojan Ruwa

Kalli Bidiyon wasannin Barkwancin da aka fito dasu dan tsokanar Ministan Abuja, Nyesom Wike biyo bayan Tirka-Tirkar da yayi da sojan Ruwa

Duk Labarai
Biyo bayan Tirka-Tirkar data faru tsakanin Ministan Abuja, Nyesom Wike da Sojan Ruwa, da ya hanashi shiga wani fili a Abuja, wasu sun rika yin wasannin Barkwanci dan tsokanar Ministan. Kalli Bidiyon wasannin Barkwancin kala-kala. https://twitter.com/PoojaMedia/status/1988549632952058286?t=ccTdSosFTEtPOikVvs0z_w&s=19 https://twitter.com/dammiedammie35/status/1988549108601106647?t=1gJd4DL3a_cKe1GOtSje8A&s=19
Bidiyon Dansandannan ya yadu sosai bayan da yace duk Sojan da ya ke ji shi kwallon Shyege ne ya je yawa ‘yansandan Rundunar ‘Police Special Forces’ rashin kunya yaga yanda zata kare tsakaninsu

Bidiyon Dansandannan ya yadu sosai bayan da yace duk Sojan da ya ke ji shi kwallon Shyege ne ya je yawa ‘yansandan Rundunar ‘Police Special Forces’ rashin kunya yaga yanda zata kare tsakaninsu

Duk Labarai
Wannan dansandan ya dauki hankula bayan da aka ganshi a wani Bidiyo yana fadin cewa, duk sojan da yake ji da kansa, ya je ya tunkari 'yansandan Rundunar 'Police Special Forces' yaga yanda zata kare tsakaninsu. Hakan na zuwane bayan dambarwar da ta faru tsakanin Ministan Abuja Nyesom Wike da wani sojan ruwa. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1988500920787702008?t=CMYjoEZwv6skU3g7NKuZAw&s=19
Dan majalisar Wakilai daga jihar Kano, Hon. Sagir Ibrahim Koki ya bar jam’iyyar NNPP

Dan majalisar Wakilai daga jihar Kano, Hon. Sagir Ibrahim Koki ya bar jam’iyyar NNPP

Duk Labarai
Dan majalisar wakilai, Hon. Sagir Ibrahim Koki ya bar jam'iyyar NNPP. Ya sanar da hakanne a wata sanarwa da ya fitar ranar 11 ga watan Nuwamba inda yace yana godiya da damar da jam'iyyar ta bashi yayi takara a cikin ta. Saidai yace dalilin na barin jam'iyyar, Rikicin Cikin gidane wanda ya hanashi gudanar da ayyukan wakilci da aka zabeshi akansu. Zuwa yanzu dai bai bayyana jam'iyyar daya koma ba.
Kalli Bidiyon: Malamai ‘yan Izala na yin kira ga matasa ‘yan Izala da su daina Yin Murna akan rasuwar Mahaifiyar Malam Abulfatahi ko cewa tana Whuta

Kalli Bidiyon: Malamai ‘yan Izala na yin kira ga matasa ‘yan Izala da su daina Yin Murna akan rasuwar Mahaifiyar Malam Abulfatahi ko cewa tana Whuta

Duk Labarai
Rasuwar malamin Addinin Islama, Dan Dariqa, Abulfatahi Sani Tijjani ta zo da cece-kuce. Mahaifiyar tasa ta rasu kuma an yi jana'izar ta kamar yanda addinin Addinin Musulunci ya tanada. https://www.tiktok.com/@nasiru.sani89/video/7571482873237277970?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7571482873237277970&source=h5_m&timestamp=1762946754&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7568740291232040721&share_link_id=22e2e33d-6163-4ccc-bb3e-eaa897bc967c&share_app_id=1233&ugbiz_name=...
Da Duminsa: Ministan Abuja, Wike ya hana ma’aikatan Hukumar kula da babban birnin tarayya Abuja amfani da wayar hannu bayan da Bidiyon rikicinsa da sojan ruwa ya yadu

Da Duminsa: Ministan Abuja, Wike ya hana ma’aikatan Hukumar kula da babban birnin tarayya Abuja amfani da wayar hannu bayan da Bidiyon rikicinsa da sojan ruwa ya yadu

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya haramta amfani da wayar hannu bayan da Bidiyon rikicinsa da wani soja ya bayyana. A wata sanarwa da aka fitar a ma'aikatar ta kula da babban birnin tarayya Abuja, tace daga ma'aikaci na mataki na 14 zuwa kasa, kada a sake ganin wani ya je wajan aiki da wayarsa. Sahara Reporters tace lamarin ya kawo rudani a ma'aikatar inda da yawan ma'aikatan hukumar abin ya basu mamaki. Tuni dai kungiyoyin fafutuka dana kare hakkin bil'adama suka rika Allah wadai da wannan mataki da kuma fadin cewa dakile fadar albarkacin bakine.
Ta yiwa Dangin Tsohon Mijinta Gargadin kada su rabata da Diyarta a Tiktok, saidai da yawa na tambayar Dangin Tsohon Mijin nata na yin Tiktok ne?

Ta yiwa Dangin Tsohon Mijinta Gargadin kada su rabata da Diyarta a Tiktok, saidai da yawa na tambayar Dangin Tsohon Mijin nata na yin Tiktok ne?

Duk Labarai
Wannan matar ta wallafa Bidiyo inda take yiwa Dangin tsohon Mijinta gargadi a Tiktok cewa su kiyayi kokarin rabata da Diyarta. Saidai da yawa na ganin cewa ba ta hanyar Tiktok ne ba ya dace ta aika da irin wannan sakon ba. https://www.tiktok.com/@694418salma/video/7571400454135926023?_t=ZS-91Kq8Av4yzh&_r=1