Friday, April 25
Shadow

Duk Labarai

Allah Sarki: Idan baku ganni ba kawai a dora daga inda na tsaya, inada makiya da yawa>>Saurari Hirar da aka yi da Ahmad Isa(Ordinary President)

Allah Sarki: Idan baku ganni ba kawai a dora daga inda na tsaya, inada makiya da yawa>>Saurari Hirar da aka yi da Ahmad Isa(Ordinary President)

Duk Labarai
Shugaban gidan Rediyon Berekete Family Ahmad Isa wanda aka fi sani da Ordinary President ya fito yayi magana bayan dadewa da aka yi ba'a ji duriyarsa ba. Mutane da yawa sun damu da rashin ji daga gareshi i da aka rika yada labaran cewa bashi da lafiyane. Saidai a wata hira da aka yi dashi wadda ta rika yawo, an jishi yana cewa, idan ba'a ganshi ba a ci gaba daga inda ya tsaya. Saurari hirar a nan https://www.tiktok.com/@yarbaba68/photo/7496424141969427729?_d=secCgYIASAHKAESPgo8rHIAL2YVd0%2B5JzFbG%2BKNkWRQVo%2BiAoJJQNPdStnG0r%2B1Fkd9aSsX63PcmniZLjfIz1zw%2FO9ges2x%2B9WLGgA%3D&_r=1&_svg=1&aweme_type=150&checksum=c4b529189383f2bd9f7b9976cd0c2badbf021874b96303fbbec873cca56e8895&cover_exp=v1&link_reflow_popup_iteration_sharer=%7B%22click_empty_to_play%22%3A1%...
INEC Na Duba Yiwuwar Bai Wa ’Yan Najeriya Damar Kada Kuri’a Ba Tare da Katin Zabe (PVC) Ba

INEC Na Duba Yiwuwar Bai Wa ’Yan Najeriya Damar Kada Kuri’a Ba Tare da Katin Zabe (PVC) Ba

Duk Labarai
INEC Na Duba Yiwuwar Bai Wa ’Yan Najeriya Damar Kada Kuri’a Ba Tare da Katin Zabe (PVC) Ba. Hukumar Zabe ta Ƙasa (INEC) tana nazarin sabon tsari da zai bai wa ’yan ƙasa damar kada kuri’a ba tare da katin zabe na dindindin (PVC) ba a babban zaɓen 2027. A cewar hukumar, sabon tsarin zai dogara ne da amfani da fasahar zamani kamar BVAS (Bimodal Voter Accreditation System) da kuma takardun tantancewa da za a iya saukewa daga shafin INEC. Wannan zai rage wahalhalu, rage kashe kuɗi, da hana saye da satar katin zabe. Sai dai, kafin wannan tsari ya fara aiki, ana buƙatar gyara dokar zabe wanda ya shafi Majalisar Dokoki domin samun doka da izinin amfani da tsarin. Wannan mataki na INEC na nuni da kokarinta wajen saukaka tsarin zabe da kara amfani da fasaha don tabbatar da gaskiya da...
Nan da shekarar 2027 za’a samu karin Talakawa a Najeriya>>Inji Bankin Duniya

Nan da shekarar 2027 za’a samu karin Talakawa a Najeriya>>Inji Bankin Duniya

Duk Labarai
Bankin Duniya ya bayyana cewa talauci a Najeriya zai karu da kaso 3.6 a cikin 100 nan da shekaru 5 masu zuwa. Bankin Yace hakan zai farune duk da ci gaban da aka samu ta fannin tattakin Arziki. Bayan Najeriya akwai kuma kasashe irin su DR. Congo da suma ake tsammanin zasu fada cikin wannan matsanancin hali. Lamarin dai na zuwane a daidai lokacin da matsalar tsaro ke kara ta'azzara a tsakanin jihohin Arewa.
Ji yanda wani mutum kan zargin kàshè matar ƙaninsa a Jigawa

Ji yanda wani mutum kan zargin kàshè matar ƙaninsa a Jigawa

Duk Labarai
Rundunar ƴansanda a jihar Jigawa sun ce sun kama wani mutum bisa zargin kashe matar ƙaninsa a ƙauyen Gunka da ke karamar hukumar Jahun a jihar. Wata sanarwa da kakakin ƴansandan jihar SP Lawan Shiisu Adam ya fitar ranar Alhamis, ya ce ana zargin mutumin mai suna Buhari Sule mai shekara 25 da far wa matar ƙanin nasa - inda ya lakaɗa mata shegen duka har ta kai ga mutuwarta. Sai dai ya ce ana tunanin cewa ba shi da lafiyar kwakwalwa, saboda baya ga kashe matar, ya kuma raunata ɗiyar makwabciyarsa ta hanyar yi mata duka da taɓarya. Sanarwar ƴansandan ta ce lamarin ya faru ne ne ranar Laraba, 23 ga watan Afrilu da misalin karfe 5:30 na yamma a ƙauyen na Gunka. "Bayan da muka je wurin da lamarin ya faru ne muka garzaya da waɗanda lamarin ya rutsa da su zuwa babban asibitin Jahun dom...
Sojojin Najeriya sun dakile yunkurin kai hàrì tare da kàshè ɗan bindiga a Filato

Sojojin Najeriya sun dakile yunkurin kai hàrì tare da kàshè ɗan bindiga a Filato

Duk Labarai
Rundunar sojin Najeriya ta Operation Safe Heaven ta ce ta daƙile wani yunkurin kai hari a ƙauyen Teegbe da ke karamar hukumar Bassa na jihar Filato, tare da kashe ɗaya daga cikin maharan. Sanarwar da mai magana da yawun rundunar Manjo Samson Nantip Zhakom ya fitar ranar Alhamis, ya ce lamarin ya faru ne ranar Laraba 23 ga watan Afrilu, inda artabun da sojojin suka yi da maharan ne ya janyo wasu suka tsere. "Wani mazaunin yankin ne ya kira mu ya faɗa mana abin da ke faruwa, daga nan dakarun mu suka garzaya wurin. Sun fafata da ƴan bindigar har ta kai ga kashe ɗaya daga cikinsu, tare da kama wasu mutum biyu waɗanda ake ci gaba da bincike a kansu," in ji Manjo Samson. Ya ƙara da cewa dakarun sun kuma samu nasarar kama wasu ƴan fashi uku a wani samame da suka kai hanyar Katnan- Burata...
Ma’aikatan Nimet sun janye yajin aiki

Ma’aikatan Nimet sun janye yajin aiki

Duk Labarai
Ƙungiyar ma'aikatan hukumar kula da yanayi ta Najeriya, NiMET sun sanar da janye yajin aikin da suka fara ranar Laraba. Ma'aikatan sun ɗauki matakin janye yajin aikin ne bayan wata ganawa da suka yi da ministan sufurin ƙasar, Festus Keyamo a Abuja yau Alhamis. Yajin aikin da suka kira kan rashin ingantaccen albashi, ya haifar da cikas a filayen jiragen sama na cikin gida - inda fasinjoji da dama suka kasa yin balaguro. Ma'aikatan sun kuma ce sun damu matuka ganin cewa ba aiwatar musu da albashi mafi ƙanƙanta da gwamnatin tarayya ta amince da shi ba.
JARUMAR MATA: Tà Çàķawa Ķwàrtòn Da Ya Yi Yùnkùrin Yi Màťà Fýadè Wùķa A Garin Jòs

JARUMAR MATA: Tà Çàķawa Ķwàrtòn Da Ya Yi Yùnkùrin Yi Màťà Fýadè Wùķa A Garin Jòs

Duk Labarai
JARUMAR MATA: Tà Çàķawa Ķwàrtòn Da Ya Yi Yùnkùrin Yi Màťà Fýadè Wùķa A Garin Jòs. {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Daga Aminu Lawal Hassan Wannan Halima Ibrahim 'ýa ta ce, mahaifinta Alh Ibrahim kanina (cousin) ne, su na zaune garin Jos. Shekaran jiya barawo ya shiga gidanta da rana ya yi ma ta sata sannan ya nemi ya yi ma ta fýaďè ta ki, shine ya sa wùķa ya nemi ya yi mata ýañķan rago Allah Ya tsare, amma ya ji ma ta çìwo a wuya, ita kuma cikin ikon Allah ta kwace wukar ta soke shi a ciki. Yanzu haka tana...
GWAMNATI ZA TA BA MAHAJJATA KUƊIN GUZIRINSU A HANNU

GWAMNATI ZA TA BA MAHAJJATA KUƊIN GUZIRINSU A HANNU

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta sanar cewa za a bai wa mahajjatan ƙasar kuɗin guzirinsu a hannu maimakon amfani da kati ko kuma asusun banki. Wata sanarwa daga ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ta ce shi ne ya nema wa mahajjatan sauƙin daga Babban Bankin Najeriya CBN. "An bayyana damuwa game da tsarin da CBN ya sharɗanta na kowane mahajjaci ya yi amfani da katin banki a matsayin wanda zai iya kawo tarnaƙi ga tsari da aikin gudanar da Hajjin 2025," in ji sanarwar da Stanley Nkwocha ya fitar. Ta ambato kwamashinan tsare-tsare da ayyukan kuɗi na hukumar alhazai, Aliu Abdulrazaq, na cewa hakan zai bai wa mahajjan Najeriya damar kashe da hannunsu yayin ibadar a Saudiyya. "Tun kafin yanzu mun sha yin ganawa game da kuɗin guziri a aikin Hajjin na 2025. Daga baya mataimakin shugab...