Friday, March 6
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Yanda matan sojojin da aka kama da zargin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki suka fito zàngà-zàngà

Kalli Bidiyon: Yanda matan sojojin da aka kama da zargin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki suka fito zàngà-zàngà

Duk Labarai
Matan sojojin da aka kama da zargin cewa sun shirya yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki sun fito zanga-zanga. Sun fito inda suka rika bayyana damuwarsu bisa jagorancin Omoyele Sowore. Sowore ya bayyana cewa da yawa iyalan sun ce babu wata maganar juyin mulki da mazajensu ke da hannu akai. Kawai wasu manyan sojoji ne ke son farantawa shugaban kasa rai. https://twitter.com/i/status/2029936108570636762
Kalli Bidiyon: Da Sheikh Salihu Zaria ya kaiwa Kwamishinan ‘Yansandan jihar Yobe, CP Emmanuel Ado ziyara inda yace masa ya karbi Musulunci

Kalli Bidiyon: Da Sheikh Salihu Zaria ya kaiwa Kwamishinan ‘Yansandan jihar Yobe, CP Emmanuel Ado ziyara inda yace masa ya karbi Musulunci

Duk Labarai
Wannan Bidiyon Sheikh Salihu Zaria ne a yayin da ya kaiwa Kwamishinan 'yansanda na jihar Yobe, CP Emmanuel Ado ziyara. Ya jawo hankalinsa da cewa ya karbi Musulunci. Rahotanni sun bayyana cewa, wannan Bidiyon na daga cikin wadanda suka sa kungiyar Izala ta dakatar da Malam Salihu Zaria daga wa'azi. https://www.tiktok.com/@youngalkaligombe/video/7613755621866835208?_r=1&_t=ZS-94SWTFYVWXA
Tsohuwar Ministar sufurin jiragen sama, Stella Oduah ta amince ta dawo da Naira Biliyan 2.5 data sata

Tsohuwar Ministar sufurin jiragen sama, Stella Oduah ta amince ta dawo da Naira Biliyan 2.5 data sata

Duk Labarai
Tsohuwar Ministar sufurin jiragen sama, Stella Oduah ta amince zata mayar da Naira Biliyan 2.5 data sata. Ta bayyana hakane a yayin zaman kotu a ranar Alhamis ita da wanda ake kararsu tare. Tace maimakon ci gaba da shari'ar, ta amince ta mayar da udaden da ta sata. Me kula da shari'ar, Rotimi Oyedepo ya tabbatar da cewa, Stella Oduah ta je ofishin babban lauyan Gwamnati kuma mw baiwa shugaban kasa shawara kan shari'a inda tace zata dawo da kudaden data sata. Hakanan shima lauyanta, Onyechi Ikpeazu, SAN, ya tabbatar da hakan inda yace suna kan kokarin dawo da kudaden. Lauyan dayan wanda ake zargi, Favour Osuanya shima yace du sun amince su mayar da kudaden. Mai shari'a, Justice Hamza Muazu ya dage shari'ar zuwa ranar 26 ga watan Maris dan jin inda aka kwana kan maganar may...
Kalli Bidiyon: Ji yanda Wani dansanda ya zangawa Sheikh Salihu Zaria Mqry

Kalli Bidiyon: Ji yanda Wani dansanda ya zangawa Sheikh Salihu Zaria Mqry

Duk Labarai
A wani Bidiyo da ya watsu a kafafen sada zumunta, an ga Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun na bada labari dalla-dalla kan dalilin dakatar da Sheikh Abubakar Salihu Zaria. Sheikh Yusuf Sambo ya bayyana cewa, DSS ne suka fara Neman Sheikh Salihu Zaria shiyasa aka dakatar dashi dan dakile fitinar. Ya kara da cewa, a baya akwai sanda aka taba kamashi, dansanda ya fallasa masa mari yace zai kara yin irin waccan maganar da yayi? Sai yace ba zai kara ba tallar Gwanjo zai koma, Sheikh Yusuf Sambo yace shine ya je ya karbo malam daga hannun jami'an tsaro. https://www.tiktok.com/@youngalkaligombe/video/7613911890586029320?_r=1&_t=ZS-94SMvR5pSWv
Allah Sarki: Ji yanda aka ga wani Kirista na sauraren wa’azin Sheikh Guruntum

Allah Sarki: Ji yanda aka ga wani Kirista na sauraren wa’azin Sheikh Guruntum

Duk Labarai
An hangi wani Kirista na sauraren wa'azin babban malamin addinin Islama, Sheikh Guruntum. Wani da ya shaida hakan ne ya fada a shafinsa na X Inda yace: "I just passed a Christian man in our area listen to Sheikh Guruntum’s Tafsir…" https://twitter.com/i/status/2029297705487327722 Wani ya bashi amsar cewa da yawa suna ji ai. https://twitter.com/i/status/2029409086475817394
Kalli Bidiyon: Labari me sanya Shauki, yanda wata mata data saba ciyar da karnuka, taje wajan Biki amma tasa aka kawo musu abinci

Kalli Bidiyon: Labari me sanya Shauki, yanda wata mata data saba ciyar da karnuka, taje wajan Biki amma tasa aka kawo musu abinci

Duk Labarai
Wata mata a kasar India da ta saba ciyar da wasu karnuka kullun da dare. Wata rana ta je wajan biki bata dawo ba sai ta sayi abinci, irin wanda ake kaiwa mutum har gida a mota ko a mashin. Da dan sakon ya je kofar gidanta sai ya kirata yace ga abincin an kawo, sai tace bata nan. Sai yace a ina zai ajiye? Sai tace masa ya duba kusa da gidanta akwai wasu karnuka ya basu abincin , ta saba basu ne kuma tasan suna nan suna jiranta amma yau bata nan shiyasa tasa a kawo musu. Haka dan sakon ya nemi karnikan ya basu abincin inda ya dauki Bidiyon lamarin saboda shima abin ya burgeshi. https://twitter.com/i/status/2029418361713791166
Kuma Dai: Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya sake maka ICPC a kotu inda yake neman su biyashi diyyar Naira Biliyan 15.6

Kuma Dai: Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya sake maka ICPC a kotu inda yake neman su biyashi diyyar Naira Biliyan 15.6

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya maka hukumar yaki da rashawa, ICPC a kotu inda yake neman su biyashi diyyar naira Biliyan 15.6 saboda bata masa suna. Hakan na zuwane yayin da ICPC tace ta gano na'urar yiwa waya kutse a gidan malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Lauyoyin Malam Nasiru sun ce kalaman na ICPC abin damuwa ne kuma sun bata masa suna Dan haka El-Rufai yace wannan abu ya take masa hakkinsa na Bil'adama inda yace yana neman. Biliyan 15.6 na bata masa suna. El-Rufai yace ya baiwa ICPC awanni 24 su gaggauta biyansa wannan kudi in ba haka ba zai makasu kotu.