Da Duminsa: Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa duk da yana APC, yawa Atiku Alkawarin bashi kudi dan yayi yakin neman zaben 2027
created by photogrid
Rahotanni daga kafar peoplesgazette sun bayyana cewa, Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya gana da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar a Saudiyya.
Kafar tace wata majiya ta gaya mata cewa, Gwamna Sule yawa Atiku Alkawarin zai bashi kudi yayi yakin neman zabe sannan kuma ya bashi tabbacin shine zai ci jihar Nasarawa a zaben 2027.
Kafar tace a yanzu Atiki bashi da isassun kudin da zai yi yakin neman zabe bayan da a baya yayi takara har sau 4 ba tare da nasara ba.
Sannan a zamanin Mulkin Buhari an durkusar da kamfaninsa na Intel.








