Thursday, February 26
Shadow

Duk Labarai

Wata Sabuwa: Ana zargin Tonon Sililin da Janar Christopher Musa yawa wasu sojoji da hannu a matsalar tsaro, da kuma kalaman da yayi na cewa Talauci da Yunwa da rashin aikin yi na kara rura wutar matsalar ne suka sa aka saukeshi daga mukaminsa

Wata Sabuwa: Ana zargin Tonon Sililin da Janar Christopher Musa yawa wasu sojoji da hannu a matsalar tsaro, da kuma kalaman da yayi na cewa Talauci da Yunwa da rashin aikin yi na kara rura wutar matsalar ne suka sa aka saukeshi daga mukaminsa

Duk Labarai
A jiya ne dai shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sanar da sauke Janar Christopher Musa daga mukaminsa na Shugaban sojojin Najeriya. Saidai rade-radin na yawo cewa, Saukeshin na da alaka da siyasa. Domin a baya ya bayyana cewa akwai wasu sojoji dakewa kokarin Gwamnati na kawo karshen matsalar tsaron zagon kasa. Hakanan ya roki gwamnati ta kawo karshen matsalar Yunwa, Talauci da rashin aikin yi wanda yace suna taimakawa rura wutar matsalar tsaro a Najeriya. https://twitter.com/Edrees4P/status/1981856038585610540?t=LQsIPBwiNJxNfXZmcFOkSQ&s=19
Kuma Dai: Bayan sauke shuwagabannin tsaro da shugaba Tinubu yayi jiya, za kuma a tursasawa Wasu manyan Janarorin soja 60 ajiye aiki

Kuma Dai: Bayan sauke shuwagabannin tsaro da shugaba Tinubu yayi jiya, za kuma a tursasawa Wasu manyan Janarorin soja 60 ajiye aiki

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa akwai karin sojoji da zasu bar aiki a Najeriya bayan da shugaba Tinubu ya sauke shuwagabannin tsaron a jiya. Rahoton wanda Daily Trust ta kawo yace manyan sojoji dake sama da sabbin sojojin da aka baiwa mukaman shugabancin gidan sojan dole su ajiye aiki. Rahoton yace dama haka tsarin aikin gidan sojan yake dan a ci gaba da samun da'a da yiwa na gaba biyayya. Hakan na zuwane sati daya bayan da rahotanni suka ce an yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu juyin mulki.
Kalli Bidiyon: Yanda Saurayi dan Kaduna ya kai Budurwarsa ‘yar Kano suka ci tsire suka kuma yi sayayya amma ya tsere ya barta

Kalli Bidiyon: Yanda Saurayi dan Kaduna ya kai Budurwarsa ‘yar Kano suka ci tsire suka kuma yi sayayya amma ya tsere ya barta

Duk Labarai
Wannan wata 'yar Kano ce da saurayinta ya kaita wajan sayayya suka ci tsire kuma suka sayi kaya amma da aka zo biyan kudi sai ya tsere. Daga baya dai sai wayarta aka kwace a shagon. Ta bayyana cewa Samarin Kaduna akwai yaudara. https://www.tiktok.com/@mix_muhammad/video/7564905876197264660?_t=ZS-90qH1uLi8DB&_r=1
Kalli Bidiyo: Naira Miliyan 2 Soja Boy yake baiwa ‘yan mata suna rawa dashi a wakokinsa na Badhala

Kalli Bidiyo: Naira Miliyan 2 Soja Boy yake baiwa ‘yan mata suna rawa dashi a wakokinsa na Badhala

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Naira Miliyan 2 Soja Boy ke baiwa wasu daga cikin 'yan matan da yake rawar badala dasu a cikin bidiyonsa. 'Yar Fim Mashahuriyace ta bayyana haka a wani Bidiyo data saki inda tace ya baiwa Eshat Aminu amma tace tafi karfin hakan. Ana dai ganin Soja Boy yana rawa da mata kala-kala inda a wasu lokutan yake kama hannunsu ko kuma ya rika rungumarsu. https://www.tiktok.com/@officialsojaboyy/video/7564851359137172756?_t=ZS-90qGa2OqrVB&_r=1
Kalli Bidiyon:Yanda dan Shugaban kasa, Seyi Tinubu ya gaisa da diyar tsohon shugaban kasa, Zahra Buhari, sannan ya Sumbhachi kanwarta

Kalli Bidiyon:Yanda dan Shugaban kasa, Seyi Tinubu ya gaisa da diyar tsohon shugaban kasa, Zahra Buhari, sannan ya Sumbhachi kanwarta

Duk Labarai
Bidiyon dan shugaban kasa, Seyi Tinubu yana gaiwa da diyar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari sannan ya sumbaci daya ya jawo cece-kuce sosai. A Bidiyon, an ga Yusuf Buhari a zaune inda Seyi ya Mikawa Zahara Buhari hannu suka gaisa sannan ya zagaya ya sumbaci 'yar uwarta. Lamarin dai ya jawo zazzafar Muhawara inda wasu ke cewa masu kudi ba ruwansu da haramun wajan gaisawa da mata. https://www.tiktok.com/@abkblogg/video/7564937419531799815?_t=ZS-90qCo7nGDZZ&_r=1
Lokacin da zan sauka daga Mulki, An so in dauko Nasiru El-Rufai a matsayin magajina, amma nace ban yadda ba sai ya Kara hankali tukuna>>Tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo

Lokacin da zan sauka daga Mulki, An so in dauko Nasiru El-Rufai a matsayin magajina, amma nace ban yadda ba sai ya Kara hankali tukuna>>Tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa, a lokacin da ya so sauka daga Mulki, an bashi shawarar ya dauko Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a matsayin magajinsa. Yace amma a wancan lokacin yaki yadda da wannan shawarar. Yace dalili kuwa shine yace Sai El-Rufai ya kara hankali. Yace da wanda ya bashi shawarar ya ga irin ayyukan El-Rufai yake yi shine ya sake zuwa ya sameshi yace lallai ya yadda da maganarsa. El-Rufai dai yayi ministan Abuja a zamanin mulkin Tsohon shugaban kasar.
An kama wani dalibi a jihar Naija saboda zargin sukar Gwamnan Jihar

An kama wani dalibi a jihar Naija saboda zargin sukar Gwamnan Jihar

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Naija na cewa, an kama wani dalibin jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida University saboda zargin ya soki gwamnan jihar, Mohammed Umar Bago. Sunan dalibin da aka kama Abubakar Isah Mokwa kuma an kamashine ranar Alhamis a dakinsa dake garin Lapai. An kamashine bayan da yayi rubutu yana sukar Gwamnan Gwamnan a shafinsa na Facebook. Kakakin 'yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun ya tabbatar da kamen inda yace suna kan binciken wanda akw zargin.
Daga aika abokina ya gwada Budurwata yace yana sonta dan in gane ko da gaske tana sona, Yanzu in gajarce muku zance ya aureta>>Inji Usman Zannah

Daga aika abokina ya gwada Budurwata yace yana sonta dan in gane ko da gaske tana sona, Yanzu in gajarce muku zance ya aureta>>Inji Usman Zannah

Duk Labarai
Matashi Usman Zannah ya bayyana cewa, ya aika Abokinsa ya gwada budurwar sa yace yana sonta dan ya gane ko tana sonsa da gaske. Yace a karshe abokin nasa da Budurwar sun yi soyayyar gaske harma sun haihu. Lamarin Ya dauki hankulan Mutane sosai inda wasu suka rika jajanta masa, wasu kuma suka rika masa Allah kara.