Saturday, December 13
Shadow

Duk Labarai

Karya ministan Lafiya yake, bamu janye yajin aiki ba>>Inji Kungiyar malaman Jinya(Nurse) na Najeriya

Karya ministan Lafiya yake, bamu janye yajin aiki ba>>Inji Kungiyar malaman Jinya(Nurse) na Najeriya

Duk Labarai
Kungiyar malaman jinya(Nurse) da Ungozoma (NANNM-FHI) sun bayyana cewa, basu janye yajin aikin da suka shiga ba na kwanaki 7. Kungiyar ta nesanta kanta da kalaman Ministan lafiya, Prof. Muhammad Pate wanda a dazu bayan kammala zaman tattaunawa dasu yace sun amince su janye yajin aikin. Me magana da yawun kungiyar, Omomo Tibiebi ne ya bayyana haka inda yacw yajin aikin da suka fara tun ranar Laraba har yanzu basu janye ba. Yace ba ministan ne ya ke yajin aikin ba, dan haka bashi da hurumin janye yajin aikin. Yace sai a ranar Asabar ne zasu zauna dan tattauna batun da duba irin alkawarin da gwamnatin ta musu ko abune da zasu iya amincewa dashi ko kuwa a'a.
Karanta Jadawalin shekarun Gwamnonin Najeriya, Ko Gwamnan jiharku shekarunsa nawa?

Karanta Jadawalin shekarun Gwamnonin Najeriya, Ko Gwamnan jiharku shekarunsa nawa?

Duk Labarai
Wannan Jadawalin shekarun Gwamnonin Najeriya ne: Bala Muhammed (Bauchi): 66 years Douye Diri (Bayelsa): 66 years Hope Uzodinma (Imo): 66 years Charles Soludo (Anambra): 65 years Bassey Otu (Cross River): 65 years Abdulrahman Abdulrasaq (Kwara): 65 years Abdullahi Sule (Nasarawa): 65 years Dapo Abiodun (Ogun): 65 years Ademola Adeleke (Osun): 65 years Muhammad Yahaya (Gombe): 63 years Sheriff Oborevwori (Delta): 62 years Umar Namadi (Jigawa): 62 years Abba Kabir Yusuf (Kano): 62 years Umo Eno (Akwa Ibom): 61 years Alex Otti (Abia): 60 years Babajide Sanwo-Olu (Lagos): 60 years Lucky Aiyedatiwa (Ondo): 60 years Caleb Mutfwang (Plateau): 60 years Nasir Idris (Kebbi): 59 years Dauda Lawal (Zamfara): 59 years Hyacinth Alia (Ben...
Da Duminsa: Kasar Amurka ta Laftawa Najeriya sabon Haraji

Da Duminsa: Kasar Amurka ta Laftawa Najeriya sabon Haraji

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa kasar Amurka ta Laftawa Najeriya sabon harajin kaso 15 cikin 100. Hakan na zuwane bayan da kwanaki 90 da kasar ta Amurka ta ware dan tattaunawar huldar kasuwanci da Najeriya ta kusanto. A watan Afrilu kasar Amurka ta kakabawa Najeriya harajin kasuwanci na kaso 14 cikin 100. Saidai a wannan sabuwar sanarwar an sabunta tare da kara kaso 1 inda ya koma kaso 15 cikin 100. Lamarin dai ba Najeriya kadai ya shafa ba hadda sauran kasashen Duniya da dama.
Kalli Bidiyon: Gwamnan Adamawa ya baiwa me horas da ‘yan wasa na Kungiyar kwallon kafa ta mata ta Najeriya Kyautar gida me dakuna 3 da Naira Miliyan 50

Kalli Bidiyon: Gwamnan Adamawa ya baiwa me horas da ‘yan wasa na Kungiyar kwallon kafa ta mata ta Najeriya Kyautar gida me dakuna 3 da Naira Miliyan 50

Duk Labarai
Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri ya baiwa Kocin kungiyar kwallon kafa ta mata ta Najeriya, Super Falcons, Justin Madugu kyautar gida da Naira Miliyan 50. Ya bashi kyautar ne a gidan gwamnatin jihar Adamawa. Ya bashi kyautar saboda kokarin da yayi na kai 'yan matan suka lashe kofin Afrika na mata wanda suka buga wasan karshe da kasar Morocco. Suma dai 'yan matan kowacce gwamnatin tarayya ta basu kyautar Naira Miliyan 152 da kuma gidaje. Sannan gwamnoni sun basu kyautar Naira Miliyan 10 kowacce. https://twitter.com/thecableng/status/1951307863176905132?t=5AnXPDT8jRDv8S2xlBvkog&s=19
Kalli Bidiyo: Su Bala Lau ‘yan Tawayene, Sheikh Sani Yahya Jingir shine shugaban Izala na gaskiya>>Inji Sheikh Musa Salihu Alburham

Kalli Bidiyo: Su Bala Lau ‘yan Tawayene, Sheikh Sani Yahya Jingir shine shugaban Izala na gaskiya>>Inji Sheikh Musa Salihu Alburham

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama Sheikh Misa Salihu Alburham ya bayyana cewa, Sheikh Sani Yahya Jingir shine shugaban Izala na gaskiya. Inda ya kara da cewa, Su Sheikh Bala Lau 'yan Tawayene. Ya bayyana hakane a wani faifan Bidiyon sa sa ya watsu sosai a kafafen sadarwa. https://www.tiktok.com/@darul_burhan_majlis/video/7532275234850852102?_t=ZS-8yWF1N9LLGL&_r=1
Da Duminsa: Malaman Jinya(Nurse) sun janye yajin aikin da suke

Da Duminsa: Malaman Jinya(Nurse) sun janye yajin aikin da suke

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, yajin aikin da malaman Jinya na Asibiti, watau Nurse suka shiga a karkashin kungiyarsu me suna (NANNM) ya zo karshe. Ministan Lafiya, Professor Ali Pate ne ya bayyana hakan bayan ganawa da wakilan malaman jihar, Nurse a ranar Juma'a. Saidai wakilan malaman jinyar sun ki cewa uffan bayan kammala zaman. A baya dai malaman jinyar sun shiga yajin aikin kwanaki 7 na gargadi.
Rundunar sojin ruwan Najeriya za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya za ta kafa sansani a Kebbi

Duk Labarai
Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta a garin Yauri na jihar Kebbi a wani mataki na bunƙasa harkokin tsaron iyakokin ruwa. Matakin na zuwa ne bayan da wata tawagar manyan jami'an sojojin ruwan suka kai ziyara gidan gwamnatin jihar Kebbi a ranar Alhamis. Tawagar ƙarƙashin jagorancin Rear Admiral Patrick Nwatu - wanda ya wakilci babban hafsan sojin ruwan ƙasar ta ziyarci Kebbi ne domin duba yadda za ta samar da sansaninta a jihar. Rundunar ta ce ta ɗauki matakin ne domin faɗaɗa ayyukanta zuwa sauran yankunan ƙasar, musamman domin samar da tsaro a kan iyakokin ƙasar na tudu da na ruwa domin magance ayyukan ɓata-gari a kogin Niger. “Duk da irin muhimmanci da kogin Niger ke da shi wajen haɓaka ayyukan noma da samar da lantarki da kamun kifi da sauran sana'o...
Tinubu ya nemi gwamnoni su haɗa hannu don yaƙi da talauci a ƙauyuka

Tinubu ya nemi gwamnoni su haɗa hannu don yaƙi da talauci a ƙauyuka

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya buƙaci gwamnonin ƙasar su fitita walwalar ƴan Najeriya ta hanyar zuba jari a ƙauyuka da yankunan karkara, ta hanyar bunƙasa wutar lantarki da ayyukan noma domin kawar da talauci. Kiran na zuwa ne bayan gabatar da wani shirin gwamnati na musamman kan bunƙasa tattalin arziki a matakin mazaɓu da aka yi wa laƙabi da 'Renewed Hope Ward Development Programme (RHWDP)' da ministan kasafi da tsare-tsare na ƙasar ya yi a lokacin taron majalisar tattalin arzikin ƙasar. Manufar sabon shirin na RHWDP shi ne tabbatar da bunƙasar tattalin arziki ta hanyar taimaka wa mazaɓun ƙasar 8,809 a faɗin jihohin ƙasar 36, kamar yadda wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasar ta bayyana. Shugaba Tinubu ya kuma buƙaci gwamnonin ƙasar su yi duk mai yiwuwa wajen tallafa wa rayukan...