Monday, March 2
Shadow

Duk Labarai

Goodluck Jonathan na son a sauya yadda ake zaɓen shugaban INEC

Goodluck Jonathan na son a sauya yadda ake zaɓen shugaban INEC

Duk Labarai
Tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, ya yi kira da a samar da sabon tsarin zaɓen shugaban hukumar zabe ta ƙasa (INEC), inda ya ba da shawarar kafa wani tsarin tantancewa da zaɓe mai zaman kansa don ƙara wa hukumar sahihanci kafin zaɓen gaba na 2027. Jonathan ya bayyana wannan ra’ayi ne a ranar Laraba a Abuja, a yayin gabatar da shirin ƙasa na gyaran harkokin zaɓe, wanda Makarantar Nazarin Zamantakewa da Siyasa ta Abuja ta shirya. Kiran ya zo ne a wani lokaci na siyasa mai ɗaukar hankali, yayin da wa’adin shugaban INEC na yanzu, Prof. Mahmood Yakubu, ke ƙarewa a watan Oktoba na wannan shekara. Yakubu, wanda ya jagoranci zaɓukan 2019 da 2023, ya riga ya yi wa’adin aiki biyu, kuma zaɓen wanda zai gaje shi na janyo ƙarin hasashe a al’umma. Masana na ganin cewa wanda zai zam...
Ba na so na tsaya takara a 2027 – El-Rufai

Ba na so na tsaya takara a 2027 – El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa ba ya tunanin tsayawa takara a zaɓen ƙasar na shekara ta 2027 ba. Ya ce dawowarsa harkar siyasa kwanan nan "ba don neman muƙami ba ne, sai don tallafa wa shugabanci nagari a dukkan matakai". El-Rufai ya yi wannan bayani ne yayin wani taron siyasa a jihar Kaduna ranar Laraba. "Asalin shirina bayan barin gwamna a 2023 shi ne na huta daga siyasa, amma abubuwan da suka faru kwanan nan ne suka tilasta min dawowa, ba don kaina ba, amma domin na bayar da goyon baya," in ji El-Rufai. El-Rufa'i ya ce "ni dai ba zan sake yin gwamna ba, ba na so na je senate (Majalisar Dattijai), ba na wata takara". Ya kuma yi kakkausar suka ga gwamnatin shugaban Najeriya Bola Tinubu, inda ya ce ta gaza. Nasir El-Rufa'i na cikin manyan ƴan...
Najeriya ta ƙara kuɗin yin fasfo

Najeriya ta ƙara kuɗin yin fasfo

Duk Labarai
Hukumar shige da fice ta Najeriya (NIS) ta sanar da ƙarin farashin yin fasafo wanda zai fara aiki daga ranar 1 ga Satumba, 2025, domin inganta inganci da tsaro a tsarin fasafo ɗin ƙasar. A cewar hukumar, farashin fasafo na shekaru biyar mai shafi 32 wanda a baya yake kan naira 70,000 yanzu zai tashi zuwa naira 100,000, yayin da na shekaru 10 mai shafi 64 wanda a baya yake kan naira 120,000 zai koma naira 200,000. Sai dai, farashin fasafo da ‘yan Najeriya ke yi a ƙasashen waje ba zai canza ba, inda za a ci gaba da biyan dala 150 kan fasafo na shekara 5 da dala 230 kan fasafo na shekara 10. Hukumar ta bayyana cewa wannan sabon tsarin na nufin tabbatar da daidaito a ayyukan fasafo, tare da sauƙaƙa damar samun fasafo ga duk ‘yan Najeriya.
Kalli Bidiyon yanda wani mutum ke bayyana cewa, yana kwanciyar aure sau 50 da matarsa a dare daya

Kalli Bidiyon yanda wani mutum ke bayyana cewa, yana kwanciyar aure sau 50 da matarsa a dare daya

Duk Labarai
Wani dan jaridar a jihar Kaduna ya bayyana cewa, akwai mutumin da ya sameshi yake gaya masa cewa yana iya kwanciya da mace sau 50 a dare daya. Yace mutumin ya sameshi ne da matarsa inda yake cewa, matarsa ta amince ya kara aure dan ta samu sauki. Saidai a gefe daya kuma an samu wacce ta yadda ya aureta amma ita tana iya kwanciyar aure sau 100 a dare daya. https://www.tiktok.com/@nahnahkhadijah1/video/7543535897908743442?_t=ZS-8zFuOyhH8DJ&_r=1
Kalli Bidiyo: Sheikh Ibrahim Maqari ya tabbatar da maganar Sheikh Ibrahim Inyas cewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) shine Mahaifin Annabi Isa(AS) na Haqiqa

Kalli Bidiyo: Sheikh Ibrahim Maqari ya tabbatar da maganar Sheikh Ibrahim Inyas cewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) shine Mahaifin Annabi Isa(AS) na Haqiqa

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Ibrahim Maqari ya tabbatar da maganar Sheikh Ibrahim Inyas cewa, Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) shine Mahaifin Annabi Isa (AS) na haqiqa. A jawabin Sheikh Maqari ya bayyana cewa irin ilimin da ake magana dashine mutane basu gane ba. Kalli Bidiyon a kasa: https://www.tiktok.com/@buharimandemgy/video/7543263229494005000?_t=ZS-8zFr0mectxQ&_r=1
HABU DAN DAMISA: Matashin Da Ya Yi Kàurin Sunà A Harkaŕ Daba A Yankin Tudun Wada Da Kewaye A Jihar Kaduna Ya Gamu Da Ajalinsa

HABU DAN DAMISA: Matashin Da Ya Yi Kàurin Sunà A Harkaŕ Daba A Yankin Tudun Wada Da Kewaye A Jihar Kaduna Ya Gamu Da Ajalinsa

Duk Labarai
HABU DAN DAMISA: Matashin Da Ya Yi Kàurin Sunà A Harkaŕ Daba A Yankin Tudun Wada Da Kewaye A Jihar Kaduna Ya Gamu Da Ajalinsa. Saidai mutuwarsa ta raba hankulan jama'a, inda wasu ke jimami wasu kuma na mùrñà, duba da yadda ya aďdabi jama'à. Ko a wani bidiyo da aka nuno kusan yara ne zalla suka yi jana'izarsa.
Sojojin Nijeriya Sun Yi Haďari A Kan Dutsen Mambilla, Dake Jihar Taraba

Sojojin Nijeriya Sun Yi Haďari A Kan Dutsen Mambilla, Dake Jihar Taraba

Duk Labarai
YANZU-YANZU: Sojojin Nijeriya Sun Yi Haďari A Kan Dutsen Mambilla, Dake Jihar Taraba. Sojoji huɗu sun jikkata a wani haɗarin mota da ya afku a Dutsen Mambilla da ke jihar Taraba. Lamarin ya faru ne a yayin da dakarun ke tsaka da tafiya a cikin tsaunukan yankin. Mai Martaba Dr. Shehu Audu Baju, Sarkin Mambilla, ya nuna ƙwarin gwiwa da tausayinsa ta hanyar sa hannu a ceto sojojin da suka samu rauni. Bayan an ceto su, an garzaya da su Barikin Sojoji na 20 Battalion da ke Serti domin samun kulawar gaggawa. Muna addu’ar Allah Ya ba su lafiya, Ya kuma kare sauran jami’an tsaro da ke bakin aiki.
Sabon Rikici ya kunno kai a jam’iyyar ADC inda tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar yace ya tsige David Mark daga shugabancin jam’iyyar

Sabon Rikici ya kunno kai a jam’iyyar ADC inda tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar yace ya tsige David Mark daga shugabancin jam’iyyar

Duk Labarai
Tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar ADC wanda ya sauka David Mark ya hau, watau Ralph Nwosu ya fito ya bayyana cewa, shine shugaban jam'iyyar ADC ba David Mark ba. Ya bayyana hakane a wani Bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta. Yace a doka idan shuaban jam'iyya ya sauka, mataimakinsa ne ke zama shugaba, dan hak shine sabon shugaban jam'iyyar ADC ba David Mark ba. https://twitter.com/AIT_Online/status/1960707243705352328?t=7Qd2ppcQoPqMaIZO8A3omA&s=19
Kalli Hotuna: Kamfanin kere-kere na Sojojin Najeriya, DICON ya bayyana Bìndìgà ta farko da ya kera

Kalli Hotuna: Kamfanin kere-kere na Sojojin Najeriya, DICON ya bayyana Bìndìgà ta farko da ya kera

Duk Labarai
Kamfanin kere-kere na sojojin Najeriya, DICON ya bayyana Bindigar yaki ta farko da ya kera. Kamfanin ya bayyana hakane a matsayin ci gaba da kuma rage dogaro da kasashen waje waja samar da makamai. Masu sharhi na bangaren tsaro sun bayyana cewa, wannan ba karamin ci gaba bane. 'yan Najeriya da yawa sun bayyana farin ciki da wannan labari inda suka ce ya kamata a samar da Bindigar da yawa ta yanda sojoji zau rika amfani da ita wajan yaki.