Saturday, May 24
Shadow

Duk Labarai

Hoto: Wannan matashin ya yi garkuwa da kansa ya karbi Naira Miliyan 5 daga gurin mahaifinsa

Hoto: Wannan matashin ya yi garkuwa da kansa ya karbi Naira Miliyan 5 daga gurin mahaifinsa

Tsaro
Wannan wani matashine dan kimanin shekaru 20 wanda ya yi garkuwa da kansa. https://www.youtube.com/watch?v=QMoREHNRpDM?si=Z_vLHKGDPEAc2llB Matashin dai ya jada baki da wanine inda aka kamashi aka daure aka kuma rika dukansa. An nemi mahaifinsa ya biya Naira Miliyan 50 wanda daga baya aka ce ya biya Miliyan 5 ta hanyar Bitcoin. Bayan biyan kudin, asirin matashin ya tonu:

Alamomin cikin wata takwas

Duk Labarai, Haihuwa, Laulayin ciki
A yayin da cikinki ya kai watanni 8, abinda ke cikinki ya kai tsawon 11 inches. A daidai lokacinne wani gashi me laushi dake lullube da abinda ke cikinki zai fara zubewa. Idan namiji ne, a wannan lokacinne marainansa zasu zazzago kasa. A wannan watanne zaki rika jin gajiya, sannan zaki rika nishi da kyar. Jijiyoyi zasu iya fitowa rado-rado musamman a kafarki. Zaki iya samun nankarwa. Zafin kirji ko zafin zuciya na iya ci gaba, hakanan zaki iya ci gaba da fama da wahala wajan yin kashi. Fitsari zai iya zubowa yayin da kika zo yin atishawa ko kuma kike dariya. Wadannan abubuwanne zaki yi fama dasu yayin da cikinki ya kai watanni 8.
Shin matakan tsuke bakin aljihun CBN na tasiri wajen rage hauhawar farashin kaya a Najeriya?

Shin matakan tsuke bakin aljihun CBN na tasiri wajen rage hauhawar farashin kaya a Najeriya?

Duk Labarai
Bankin duniya ya bayyana damuwa tare da kokwanto game da irin matakan tsuke bakin aljihu da babban bankin Najeriya yake dauka, domin shawo kan matsalar hauhawar tashin farashin kayayyaki da kasar ke fama da shi. Cikin wani rahoto da bankin ya fitar, ya ce duk da irin matakan da Babban Bankin Najeriya CBN ke dauka kamar kara kudin ruwa a bankuna, har yanzu bata sauya zani ba. Tuni dai masana tattalin arziki a Najeriya suka fara tsokaci kan rahoton Bankin Duniyar. Dakta Murtala Abdullahi Kwara, masanin tattalin arziki ne, ya shaida wa BBC cewa, Bankin Duniya ya san da ma duk wasu tsare tsare da matakai da CBN ke dauka ba lallai su yi tasiri wajen magance hauhawar farashin kayayyaki ba. Ya ce,”Dalilin da ya janyo haka kuwa shi ne kusan rabin tattalin arzikin Najeriya ya dogara ne ...

Alamomin ciwon ulcer

Duk Labarai
Menene cutar Ulcer? Cutar ulcer ko gyambon ciki, kamar yanda aka fi saninta da Hausa, ciwone dake samuwa a cikin dan adam ko kuma a cikin hanjinsa. Allah ya halicci wata kariya a cikin dan Adam. Kariyarce idan ta samu matsala, sai wasu sinadarai da jikin mutum ke samarwa na sarrafa abinci su ji mada ciwo a ciki ko a hancinsa. Ana iya maganin cutar ulcer cikin sauki. Amma idan aka barta ba tare da kulawa ba, tanawa mutum illa sosai. Abubuwan dake kawo cutar ulcer Abubuwan dake kawo cutar ulcer sun hada da: Cutar da Bakateriya ke sawa. Yawan shan magungunan Aspirin, ibuprofen, da naproxen. A likitance, abinci baya saka ulcer. Alamomin ciwon Ulcer Alamar ciwon ulcer ya danganta da tsananin ciwon. Mafi shaharar alamar ciwon ulcer itace jin zafi a tsakanin kirji ...
CIKIN HOTUNA: Rarara Ya Tallafawa Wasu daga cikin kin manoman Jihar Katsina, da Naira Miliyan Ashirin ( 20,000,000 ) Domin Suyi Chefanen Babbar Sallah

CIKIN HOTUNA: Rarara Ya Tallafawa Wasu daga cikin kin manoman Jihar Katsina, da Naira Miliyan Ashirin ( 20,000,000 ) Domin Suyi Chefanen Babbar Sallah

Duk Labarai
CIKIN HOTUNA: Rarara Ya Tallafawa Wasu daga cikin kin manoman Jihar Katsina, da Naira Miliyan Ashirin ( 20,000,000 ) Domin Suyi Chefanen Babbar Sallah. Anyi Taron Bada Tallafin Ne a Garin Kahutu Karamar Hukumar Danja Dake Jahar Katsina. Rabi'u Garba GayaMedia Aide To Dauda Adamu Abdullahi Kahutu Rarara.
Kotun Ƙolin Amurka ta amince da amfani da ƙwayoyin zubar da ciki

Kotun Ƙolin Amurka ta amince da amfani da ƙwayoyin zubar da ciki

Siyasa
Bakin Alƙalan Kotun Ƙolin Amurka yazo ɗaya wajen amincewa da amfani da ƙwayoyin zubar da ciki. Wani lamari da ake gani a matsayin nasara ga masu fafutukar 'yancin zubar da ciki. Kotun ta yi watsi da buƙatar ƙungiyoyin likitoci masu yaƙi da zubar da ciki da kuma 'yan gwagwarmaya da suke neman a taƙaita amfani da maganin Mifepristone. Kotun kolin ta ce ƙungiyoyin likitocin ba su da 'yanci shigar da ƙara kan hakan, kuma sun gaza gabatar da hujjojin cewa maganin Mifepristone yana cutarwa. Wannan ne babban hukuncin da kotun ta yanke, tun watsi da 'yancin zubar da ciki da kotun tarayyar ƙasar ta yi shekara biyu da suka gabata.

G7 ta amince a yi amfani da kadarorin Rasha da aka ƙwace a ƙasashen duniya

Siyasa
Ƙungiyar Ƙasashen G7 masu ƙarfin masana'atu sun amince a yi amfani da ribar kadarorin Rasha da aka ƙwace, domin bai wa Ukraine ta yi amfani da su. Biden ya ce yarjejeniyar za ta hada da tura bayanan sirri, da bai wa sojoji horo da bin dokokin NATO da zuba kuɗi a masana'antu da ke Ukraine domin ci gaba da samar da makamai. Biden ya ce burinsu shi ne samar wa Ukraine tsaro ''na gaske'', da kuma turmusa hancin Rasha da ƙawayenta a ƙasa. Shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz ya ce wannan ba abu ne da Shugaba Putin zai kawar da kai ya kyale ba.
Ba za mu taɓa yin sulhu da ‘yan bindiga ba – Gwamnan Zamfara

Ba za mu taɓa yin sulhu da ‘yan bindiga ba – Gwamnan Zamfara

Duk Labarai
Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawan Dare ya jaddada ƙudurin gwamnatinsa na rashin yin sulhu da 'yan bindiga. Yayin da yake gabatar da jawabi bayan ya shiga wani tattaki da ƙungiyoyin matasan jihar suka shirya a wani ɓangare na bikin ranar Dimokradiyya, Gwamnan Dauda ya ce zai yi duk abin da ya dace domin maido da jihar kan turbar zaman lafiya. ''Jiharmu na da tarihin zaman lafiya, amma sannu a hankali abubuwa suka fara taɓarɓarewa, sakamakon ayyukan ɓata-gari'', inji gwamnan. Gwamnan ya ce matsalar tsaro matsala ce da ta shafi kowa da kowa, don haka ya yi kira ga al'ummar jihar su haɗa hannu wajen tabbatar da zaman lafiyar jihar. "A koyaushe ina faɗa ina maimaitawa bai kamata ka yi sulhu da kasasshe ba, mun ga yadda gwamnatocin da suka gabata suka yi yunƙurin sulhu da 'yan bindig...
Za a ci gaba da sauye-sauyen tattalin arziƙi duk da wahalhalun da ake fuskanta – Tinubu

Za a ci gaba da sauye-sauyen tattalin arziƙi duk da wahalhalun da ake fuskanta – Tinubu

Siyasa
Shugaban Najeriya Bola Tinubu, ya ce sauye-sauyen da gwamnatinsa ta yi ya zama dole wajen gyara tattalin arzikin kasar, duk kuwa da kara wahalhalun da ake fuskanta da ke janyo fushin jama'a. Tinubu ya bayyana hakan ne a jawabinsa na jiya a yayin bikin ranar dimokuradiyyar Najeriya. “Na fahimci matsalolin tattalin arziki da muke fuskanta a matsayinmu na kasa. Tattalin arzikinmu yana cikin tsananin bukatar gyara shekaru da yawa. Ba a daidaita shi ba saboda an gina shi a kan kura-kurai na dogaro da kudaden shigar da ake samu daga hako man fetur,” inji Tinubu. Tun bayan hawansa ƙaragar mulki a bara, Tinubu ya cire da tallafin man fetur wanda ya haddasa tashin gwauron zabin sufuri da farashin abinci da sauran kayayyakin masarufi a fadin kasar. Dubban ‘yan Najeriya ne suka fito kan t...