Saturday, March 7
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa: Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya ciyo bashin Dala Biliyan 21 daga kasashen Duniya Daban-daban

Da Duminsa: Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya ciyo bashin Dala Biliyan 21 daga kasashen Duniya Daban-daban

Duk Labarai
Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya ciyo bashin Dala Biliyan 21. A ranar Talata, Majalisar Dattawa ta amince da shirin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na neman bashin waje sama da dala biliyan 21 ($21bn) domin gudanar da kasafin kudin shekarar 2025–2026, wanda hakan zai bai wa gwamnati damar aiwatar da dokar kasafin kudin 2025 gaba daya. Shirin bashin da aka amince da shi ya hada da dala biliyan 21.19 ($21.19bn) na rancen waje kai tsaye, Euro biliyan 4 (€4bn), Yen biliyan 15 (¥15bn), kyautar tallafi ta dala miliyan 65 ($65m), da kuma rancen cikin gida ta hanyar takardun bashi na gwamnati da jimillar su ta kai kusan Naira biliyan 757 (₦757bn). Haka kuma an tanadi damar tara har zuwa dala biliyan 2 ($2bn) ta hanyar amfani da kayan aikin kudi da aka bayyana da kudin waje a kasuwa...
Kalli Bidiyo: Dangote ya bayyana irin muguntar da aka masa data kusa sawa ya kasa gina matatar man fetur dinsa

Kalli Bidiyo: Dangote ya bayyana irin muguntar da aka masa data kusa sawa ya kasa gina matatar man fetur dinsa

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya bayyana irin muguntar da wani kamfani ya masa da ya bashi matsala sosai Yace a lokacin suna gina matatar man sa, sun baiwa wani kamfanin da baiso ya ambaci sunansa kwangilar kawo musu kaya. Yace kamfanin sai ya kawo kaya marasa kyau suka yi amfani dasu, yace kamin su gyara matsalar da abin ya basu sai da suka shekara 2. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1947655317292003554?t=JRkkmlNu0L_RDe7SvsYSnA&s=19
Ji Abinda Sanata Natasha Akpoti ta sake gayawa Sanata Godswill Akpabio bayan da aka hanata shiga majalisa a yau

Ji Abinda Sanata Natasha Akpoti ta sake gayawa Sanata Godswill Akpabio bayan da aka hanata shiga majalisa a yau

Duk Labarai
Sanata Natasha Akpoti ta zargi kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio da jin haushinta ya hanata ta shiga majalisar a yau saboda ta yi magana game da cin zarafinta. Ta ce kotu ta soke dakatarwar da aka mata dan haka yanzu tana da ikon shiga majalisar. Da take magana ga manema labarai a kofar majalisar, Sanata Natasha Akpoti tace ba gaskiya bane cewa wai an dakatar da ita komawa majalisar saboda daukaka kara da majalisar ta yi akan lamarin. Tace majalisar bata daukaka kara ba kan maganar komawarta majalisar. Tace hanata shiga majalisar take hakkinta ne dana mutanen mazabarta. Sanata Natasha Akpoti tace Akpabio ne kakakin majalisar Dattijai mafi muni da aka taba yi.
Manoman Najeriya na ƙaurace wa masara da shinkafa saboda tsadar taki

Manoman Najeriya na ƙaurace wa masara da shinkafa saboda tsadar taki

Duk Labarai
Manoman shinkafa da masara a Najeriya na fargabar za su iya tafka asara sakamakon tsadar taki da sauran kayan aikin noma. Wasu manoman kuwa sun hakura da noman shinkafar kacokan sun koma noman wani abu daban, saboda a cewarsu tsadar taki ba za ta bari su samu riba ba. Wannan dai na zuwa ne duk da iƙirarin da gwamnatin tarayya ta yi na cewa ta rage farashin takin zamani ga manoma a sassan ƙasar don tallafawa harkokin noma. Wani manomi a jihar Jigawa, Alh. Muhammad Idris ya shaida wa BBC cewa ya kashe kuɗi har naira miliyan ɗaya da dubu ɗari takwas wajen siyan taki da zai yi noma da shi da kuma kuɗin banruwa a kowacce kadada. "Duk da kuɗin da na kashe wajen noma, gaskiyar magana itace babu ribar da zan samu idan aka yi la'akari da tsadar taki da ya tashi da kuma shi kansa shinkaf...
Kuma Dai: Bayan Filayen da ya baiwa ‘ya’yansa, Ministan Abuja, Nyesom Wike ya sake baiwa mahaifinsa da ‘yan uwansa maza da mata da abokai tarin filaye a Abuja

Kuma Dai: Bayan Filayen da ya baiwa ‘ya’yansa, Ministan Abuja, Nyesom Wike ya sake baiwa mahaifinsa da ‘yan uwansa maza da mata da abokai tarin filaye a Abuja

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya Biwa mahaifinsa, Joshua Nlemanya Wike dan shekaru 90 fili a Abuja. Rahoton yace Wike ya baiwa mahaifin nasa filinne a Guzape II wanda darajarsa ta kai ta Naira Miliyan 400. Hakanan bayan mahaifinsa akwai 'yan uwansa maza da mata da abokai da ya baiwa filayen a Abuja. Hakan na zuwa ne kwanaki bayan da aka zargi Wike da baiwa 'ya'yansa filaye a Abujan, zargin da ya karyata yace Atiku ne ke son bata masa suna. Rahoton yace mutane 38 ne Wike ya baiwa ma'aikatansa yace a basu filaye, ma'aikatan da yawa sun yi mamakin wannan abu, kamar yanda peoplesgazette ta ruwaito.
Kalli Hotuna: Kasar Saudiyya ta bude bandaki me AC(Na’urar Sanyaya daki) ga direbobi

Kalli Hotuna: Kasar Saudiyya ta bude bandaki me AC(Na’urar Sanyaya daki) ga direbobi

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Kasar Saudiyya ta bude ban daki ga direbobi masu kai sakonni wanda ke da AC watau Na'urar sanyaya daki. An bude ban dakinne a Al Khobar kuma shine irinsa na farko.
Kalli Sabon Bidiyo da Duminsa: Duk da ta kutsa kai cikin Farfajiyar majalisar tarayya da karfin tsiya, An kulle ainahin cikin zauren Majalisar aka hana sanata Natasha Akpoti shiga ciki, yayin da su Akpabio ke ciki, Ji abinda ya kuma yi

Kalli Sabon Bidiyo da Duminsa: Duk da ta kutsa kai cikin Farfajiyar majalisar tarayya da karfin tsiya, An kulle ainahin cikin zauren Majalisar aka hana sanata Natasha Akpoti shiga ciki, yayin da su Akpabio ke ciki, Ji abinda ya kuma yi

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Bayan da ta kutsa kai da karfin tsiya cikin farfajiyar majalisar Dattijai An kuma hana Sanata Natasha Akpoti shiga ainahin cikin zauren majalisar inda su Akpabio ke zaune. Sai dai data ga haka, ita da magoya bayanta sun ja da baya sun koma inda suka fito. https://twitter.com/TheNationNews/status/1947635909077127430?t=xG8kF_D5giCzLcBcsoKGGQ&s=19 https://twitter.com/TheNationNews/status/1947635768119136434?t=ULzpUVqnpg7HZ0c8nEIhkg&s=19
Da Duminsa: Har yanzu Ina jam’iyyar PDP amma ni da jam’iyyar PDP ta jihata Shugaba Tinubu zamu zaba a zaben shekarar 2027>>Inji Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke

Da Duminsa: Har yanzu Ina jam’iyyar PDP amma ni da jam’iyyar PDP ta jihata Shugaba Tinubu zamu zaba a zaben shekarar 2027>>Inji Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke

Duk Labarai
Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai zaba a shekarar 2027. Gwamnan ya bayyana hakane bayan wani zama da aka yi tsakanin sarakunan gargajiya da manyan ma'aikatan gwamnati na jihar da sauran masu ruwa da tsaki. Gwamnan yace dukansu a jihar sun yanke shawarar goyon bayan shugaban kasa Bola Tinubu a zaben shekarar 2027 me zuwa a matsayin dansu. Gwamnan ya bayyana hakane a shafinsa na X.
Shekaruna 97 amma ban taba ganin irin gatan da shugaba Tinubu yawa gawar shugaba Buhari ba shiyasa zamu zabeshi a 2027>>Inji Sarkin Daura

Shekaruna 97 amma ban taba ganin irin gatan da shugaba Tinubu yawa gawar shugaba Buhari ba shiyasa zamu zabeshi a 2027>>Inji Sarkin Daura

Duk Labarai
Dalilan da su ka sanya za mu yi Tinubu a 2027- Sarkin Daura {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Sarkin Daura a Jihar Katsina, Umar Faruq-Umar, ya ce zai mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya ya yi tazarce a 2027 saboda girmamawar da shugaban ya yi wa masarautar Daura da kuma Jihar Katsina ta hanyar yi wa wanda ya gada, tsohon Shugaba Muhammadu Buhari, jana'izar ban-girma. Sarkin ya bayyana goyon bayansa ne a fadarsa da ke Daura a ranar Asabar yayin da ya tarbi tawagar matan gwamnonin Najeriya, ƙarƙashin jagorancin...