Sunday, December 21
Shadow

Duk Labarai

Idan da gaske kake game da daina Shigo da abubuwa daga kasashen waje a rika Amfani da wanda aka yi a Najeriya, ka ajiye motocin Alfarma da kake hawa ka koma Amfani da motocin Innoson da ake kerawa a jihar Anambra>>Atiku ya gayawa Tinubu

Idan da gaske kake game da daina Shigo da abubuwa daga kasashen waje a rika Amfani da wanda aka yi a Najeriya, ka ajiye motocin Alfarma da kake hawa ka koma Amfani da motocin Innoson da ake kerawa a jihar Anambra>>Atiku ya gayawa Tinubu

Duk Labarai
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya cewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu idan da gaske yake maganar daina amfani da abubuwan da aka kera a kasashen waje to ya daina amfani da motocin Alfarmar da yake hawa ya koma Amfani da motar Innoson da ake kerawa a jihar Anambra. Ya bayyana hakanne bayan da shugaba Tinubu ya baiwa ma'aikatun gwamnati umarnin su daina shigo da kayan da ake yin irin su a Najeriya. Saidai Atiku yace wannan duk yaudara ce wadda 'yan Najeriya sun saba ji, yace idan Gwamnatin da gaske take, ta fara daga kan kanta. Yace kamata yayi shugaba Tinubu ya fara da kanshi, ya daina amfani da motocin Alfarma da yake amfani dasu ya koma amfani da motocin Innoson ko makamantansu da ake kerawa a Najeriya. Yace ministocin Buharin ma haka ya kamata su ...
Wata Kungiyar masu ikirarin Jìhàdì ta je kusa da Abuja ta kafa sansani

Wata Kungiyar masu ikirarin Jìhàdì ta je kusa da Abuja ta kafa sansani

Duk Labarai
Kungiyar dake ikirarin jìhàdì ta Ansaru ta je kusa da babban birnin tarayya Abuja ta kafa sansani. Rahoton yace kungiyar wadda ta balle daga Bòkò Hàràm ta kuma kafa sansanoni 8 a cikin jihar Kogi. Wasu daga cikin sansanonin kungiyar na tsakanin Obajana da Kabba wanda hakan yasa manyan mutane dake wucewa ta wajan biyan kudi masu yawa dan samarwa kansu tsaro yayin wucewa ta wajan. Rahoton yace babban wajan horas da 'yan kungiyar na kilomita 93 ne tsakaninsa da babban birnin tarayya, Abuja. Kokarin jinn ta bakin hukumomin tsaro kan lamarin ya ci tura.
Ba zamu kara yadda da wani uzuri ba na rashin samar da ingantacciyar wutar Lantarki>>Ministan Wuta ya gayawa ma’aikatar wutar Lantarkin

Ba zamu kara yadda da wani uzuri ba na rashin samar da ingantacciyar wutar Lantarki>>Ministan Wuta ya gayawa ma’aikatar wutar Lantarkin

Duk Labarai
Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu ya bayyanawa ma'aikatun wutar Lantarki na kasa cewa Gwamnati ba zata sake amincewa da rashin samar da wutar lantarkin ba. Ya bayyana hakane bayan amincewa da sabon daftarin gyaran wutar. Yace kuma an samar da wani sabon tsari na baiwa ma'aikatan wutar Lantarkin horaswa ta musamman. Inda yace nan da shekaru 10 za'a magance matsalar karancin ma'aikata a hukumar wutar lantarkin.
Dattawan APC sun ce basu son Kwankwaso ya koma jam’iyyar

Dattawan APC sun ce basu son Kwankwaso ya koma jam’iyyar

Duk Labarai
Raɗe-raɗin dawowar Kwankwaso jam'iyyar APC mai mulki, na cigaba da fitowa fili. An samu rudani a sakateriyar jam’iyyar APC, a ranar Talata, bayan da Shugaban jam’iyyar na kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da Ministan Jiha na Harkokin Gidaje da Ci gaban Birane, Yusuf Ata, suka yi sabani kan daowawar Kwankwaso jam'iyyar APC. Yayin da Minista Ata ke cewa Kwankwaso – wanda kuma tsohon Ministan Tsaro ne – ya rasa karbuwa a Kano kuma siyasar sa na dab da mutuwa, Ganduje ya ce APC ba lallai ta ki karbansa ba, yana mai cewa “aboki a lokacin bukata, aboki ne na gaskiya.” Ata, yayin da yake zantawa da manema labarai bayan ganawa da Ganduje a sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, ya bayyana cewa matsin lambar siyasar da Kwankwaso ke ciki ne ke sa shi kokarin dawowa APC, yana mai cewa har Kw...
Mutane sama da dari biyu sun karbi Musulunci

Mutane sama da dari biyu sun karbi Musulunci

Duk Labarai
Mutane Sama da 210 tare da ya'yansu Sun karbi Addinin Muslunci. Fiye da mutum 210 tareda ‘ya’yansu ne suka Karbi Addinin musulinci a kauyen (Jadebri) da ke karamar hukumar (Bandai) a Arewacin Ghana. Allah ya ɗaukaka Addinin Muslunci da Musulmai Sannan Ana Bukatar Kayi Sharing Zuwa group group domin Samun Addu'o'in Al'ummar Musulmai Allah ya Dawwamar dasu a Cikin Addinin Muslunci
Gwamnan Jihar Kano ya bayar da Naira Miliyan 15 dan a ci gaba da kulawa da me cutar daji, Halisa Muhd

Gwamnan Jihar Kano ya bayar da Naira Miliyan 15 dan a ci gaba da kulawa da me cutar daji, Halisa Muhd

Duk Labarai
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Biyawa Halisa Muhd Naira Miliyan 15 Don Ci Gaba da Maganin Cututtukan da ke Damunta Mai girma Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sake nuna jajircewarsa wajen tallafawa marasa lafiya masu bukata ta musamman, inda ya biya Naira miliyan 15 domin ci gaba da maganin Halisa Muhd, wadda ke fama da cutar daji (cancer). Wannan kudin na daga cikin tallafin da Gwamnan ya bayar domin taimakawa Halisa Muhd wajen samun magani mai tsada, bayan da ya riga ya biya kudin aikin farko da aka yi mata. Fauziyya D. Sulaiman, Babbar Mai Ba Gwamna Shawara kan Harkokin Mabukata da Gajiyayyu, ta bayyana godiyarta ga Gwamnan bisa wannan taimako, tare da jaddada cewa gwamnatin Kano za ta ci gaba da tallafawa marasa lafiya da masu bukata ta musamman a jihar. Wannan ...
Atiku Abubakar ya bayyana cewa ba zai bar jam’iyyar PDP ba amma ya fadi dabarar da zasu yi amfani da ita dan kawar da Gwamnatin Tinubu

Atiku Abubakar ya bayyana cewa ba zai bar jam’iyyar PDP ba amma ya fadi dabarar da zasu yi amfani da ita dan kawar da Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Madugun Adawar Siyasa A Najeriya kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana cewa yana nan daram a cikin jam’iyyar PDP, kuma ba shi da niyyar ficewa daga cikinta. Ya bayyana hakan ne a wata ganawa da mata mambobin Kwamitin Amintattu na jam’iyyar (BoT) da suka kai masa ziyara domin neman hanyoyin ceto jam’iyyar daga rushewa gaba daya. A cewar Atiku, rahotannin da ke cewa yana shirin barin PDP zuwa wata jam’iyya kamar SDP ba su da tushe balle makama, kuma an kirkire su ne domin rikita shirin kafa kawancen jam’iyyun adawa da ake yi. Ya jaddada cewa yana nan a matsayin cikakken memba na PDP, kuma yana jagorantar yunkurin kafa kawancen jam’iyyun adawa domin kalubalantar jam’iyyar APC a zaben 2027. A wata ganawa da aka yi a Abuja, Atiku y...