Saturday, December 20
Shadow

Duk Labarai

An kàshè shanu 37 a jihar Plateau

An kàshè shanu 37 a jihar Plateau

Duk Labarai
Akalla shanu 37 aka harbe a ƙauyen Tashek da ke ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Plateau a jiya Lahadi. A cewar shugaban reshen jihar na kungiyar Miyetti Allah , Ibrahim Yusuf Babayo, lamarin ya faru ne kusan ƙarfe 1:00 na rana. Wannan harin na baya-bayan nan ya faru ne kasa da mako guda bayan wani hari makamancin haka a ƙauyen Tanjol, wanda ma yana cikin ƙaramar hukumar Riyom, inda 'yan bindiga suka budewa makiyaya wuta, suka jikkata makiyaya biyu tare da kashe shanu biyar. Shugaban kungiyar ya bayyana harin a matsayin wanda ba tare da wani dalili ba, yana mai cewa lamarin wani ƙulli ne na masu aikata hakan domin cimma wani ɓoyayyen buri. Babayo ya ce, “'Yan bindiga sun mamaye yankin suka fara harbin shanun da ke kiwo, wanda ya kai ga mutuwar shanu 37 da kuma raunata wani makiya...
Gwamnatin taraiya ta umurci WAEC da NECO su koma zana jarrabawa ta na’ura mai ƙwaƙwalwa

Gwamnatin taraiya ta umurci WAEC da NECO su koma zana jarrabawa ta na’ura mai ƙwaƙwalwa

Duk Labarai
Gwamnatin taraiya ta umurci WAEC da NECO su koma zana jarrabawa ta na'ura mai ƙwaƙwalwa. Gwamnatin Taraiya ta umurci Hukumar Shirya Jarabawa ta Afirka ta Yamma (WAEC) da Hukumar Jarabawa ta Kasa (NECO) da su fara gudanar da dukkan jarabawarsu ta hanyar amfani da Kwamfuta (CBT) daga shekarar 2026. Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ne ya bayyana hakan yayin da yake sa ido kan jarabawar da ake gudanarwa tare da jami'an JAMB, a Bwari, ranar Litinin. Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa fiye da dalibai miliyan biyu ne suka yi rajistar jarabawar da ake gudanarwa a fiye da cibiyoyi 800 a fadin kasar nan. Alausa ya bayyana cewa daga watan Nuwamba mai zuwa, WAEC da NECO za su fara gudanar da jarabawarsu ta bangaren tambayoyi (objective) ta hanyar CBT. A ...
Kwangila Kazantaccen Abu ce sam bai dace ace malami ya shiga harkar Kwangila ba a Najeriya>>Sheikh Maqari

Kwangila Kazantaccen Abu ce sam bai dace ace malami ya shiga harkar Kwangila ba a Najeriya>>Sheikh Maqari

Duk Labarai
Babban malamin addinin Islama Sheikh Ibrahim Maqari ya bayyana cewa kwagila kazantaccen abu ce da bai dace ace an samu malami yana yin ta ba. Ya bayyana hakane a wani faifan Bidiyon sa da ya watsu sosai a kafafen sadarwa. Malam yace a baya yana tunanin Shubuhar da ke cikin kwangila wani kasone, saidai yace wani masanin harkar Kwangila ya sanar dashi cewa kaso 100 bisa 100 na kwangila haka take. Yace yawanci ana bayar da itace a farashi sama dana kayan da za'a siya kuma dolene sai an baiwa wanda ya bayar da kwangilar kasonsa. Yace to irin wannan ai bai kamata ace malami ya shiga wannan harka a.
Kai ma ka taimaka wajen ƙara talauci a Najeriya’>>Gwanati ta mayarwa Peter Obi Martaninkan cewar da yayi talauci ya karu

Kai ma ka taimaka wajen ƙara talauci a Najeriya’>>Gwanati ta mayarwa Peter Obi Martaninkan cewar da yayi talauci ya karu

Duk Labarai
‘Kai ma ka taimaka wajen ƙara talauci a Najeriya’ — Sanwo-Olu ya kalubalanci Obi kan maganganunsa a jami'a a Amurka. Babajide Sanwo-Olu, gwamnan jihar Legas, ya soki Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party (LP) a 2023, kan maganganun da ya yi game da hauhawar talauci a Najeriya. A ranar Alhamis da ta gabata, Obi, tsohon gwamnan Anambra, ya yi jawabi a jami'ar Johns Hopkins a Amurka kan taken: ‘Siyasa da Sauyi a Najeriya’. A cikin jawabin, Obi ya bayyana cewa Najeriya na da mafi yawan talakawa fiye da Indonesia, China da Vietnam. Obi ya wallafa wani ɓangare na jawabin nasa a shafin X. Sanwo-Olu, a cikin wata sanarwa, ya soki Obi kan "mugun ɗabi’a" da ke "ɓata suna da darajar Najeriya a idon duniya." Gwamnan Legas ya ce la'akari da abin da Obi ya cim...
Mataimakin shuaban kasa, Kashim Shettima ya isa Jihar Delta dan karbar gwamnan jihar da ya koma APC

Mataimakin shuaban kasa, Kashim Shettima ya isa Jihar Delta dan karbar gwamnan jihar da ya koma APC

Duk Labarai
Mataimakin shuaban asa, Kashim Shettima ya isa birnin Asaba na jihar Delta dan karbar gwamna jihar, Sheriff Oborevwori da ya kom jam'iyyar APC. Gwamnonin Kaduna, Nasarawa, Kogi, Sokoto, Gombe, Legas, da Yobene suka tarbi mataimakin shugaban kasar ayan isarsa birnin Asaba. A ranar 23 ga watan Afril ne gwamna Sheriff Oborevwori ya canja sheka daga PDP zuwa APC.
Ba a ga watan Zulki’ida ba a Najeriya – Fadar sarkin Musulmi

Ba a ga watan Zulki’ida ba a Najeriya – Fadar sarkin Musulmi

Duk Labarai
Fadar Sarkin Musulmi a Najeriya Muhammad Sa'ad Abubakar III ta ce ranar Talata ce 1 ga watan Zulki'ida na shekarar Hijira ta 1446. Wata sanarwa da shugaban kwamatin ganin wata na fadar, Farfesa Sambo Wali ya fitar ta ce an ɗauki matakin ne saboda ba a ga jaririn watan ba a ranar Lahadi. A ƙa'idar kalandar Musulunci, kowane wata yana yin kwana 29 ne, amma idan ba a ga jaririn watan ba sai a cika shi zuwa kwana 30. Hakan na nufin yau Litinin 28 ga watan Afrilu ne 30 ga watan Ƙaramar Sallah na Shawwal.
Watanni 15 bayan fara biniken Tsaffin Ministocin jin kai, Sadiya Umar Farouk da Betta Edu har yanzu EFCC bata fitar da sakamakon binciken ba

Watanni 15 bayan fara biniken Tsaffin Ministocin jin kai, Sadiya Umar Farouk da Betta Edu har yanzu EFCC bata fitar da sakamakon binciken ba

Duk Labarai
A tsawon watanni 15 da suka gabata, Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Ƙasa (EFCC) bata fitar da cikakken rahoton binciken zargin almundahana da suka shafi tsofaffin Ministocin Harkokin Jinƙai, Gudanar da Bala’o’i da Ci gaban Zamantakewa — Sadiya Umar-Farouq da Betta Edu. Binciken, wanda ya kuma shafi tsohuwar Shugabar Hukumar Tsarin Tallafin Jama’a ta Ƙasa (NSIPA), Halima Shehu, da wani ɗan kwangila mai suna James Okwete, ya ci gaba da gudana a karkashin jagorancin EFCC, duk da dogon lokaci da ya wuce tun fara shari’ar. Rahotanni sun nuna cewa, sama da naira biliyan 30 (N30bn) ne aka gano an dawo da su daga asusun bankuna kusan 50 da aka alakanta da ma’aikatar lokacin da Edu da Sadiya ke rike da madafun iko, bayan haɗin guiwa tsakanin EFCC da Hukumar Yaki da Rashawa da Sauran L...
Farashin Buhun shinkafa me girman 50kg ya koma Naira Dubu 58

Farashin Buhun shinkafa me girman 50kg ya koma Naira Dubu 58

Duk Labarai
A yayin da aka fara shigo da shinkafa daga kasashen waje, misali kasar Benin zuwa Najeriya, farashin buhun shinkafa musamman a kauyuka ya koma Naira dubu 58,000. Kungiyar S&P Global ce ta fitar da wadannan bayanai inda tace farashin shinkafar a yankin Afrika ta yamma yayi faduwar da ba'a taba ganin irin ta ba tun shekaru 2 da suka gabata. Hakan na da alaka da cire harajin fitar da shinkafa zuwa kasashen waje da kasar India ta yi, kamar yanda rahoton ya nuna. Farashin shinkafar ya sauka daga Naira Dubu 80 zuwa Naira dubu 58 kan kowane buhu. Rahoton ya kara da cewa, kasar India ta ta kawo shinkafa me yawa yankin na Afrika maso yamma.
Shekarata 10 ina sana’ar sayar da sassan jikin mutane>>Inji Wannan wannan matsafin da aka kama

Shekarata 10 ina sana’ar sayar da sassan jikin mutane>>Inji Wannan wannan matsafin da aka kama

Duk Labarai
An kama wani me sana'ar sayar da sassan jikin dan Adam me suna Gani a yankin Kulanla Odomoola na jihar Ogun. Sojoji na runduna ta 81 ne suka kamashi a yayin da mutane suka rufar masa da duka ana shirin kasheshi. Ya amsa laifinsa inda yace shekara goma kenan yana wannan sana'a. Ya kara da cewa, yakan samu sassan jikin dan Adam ne a makabartu da kuma idan an yadda gawa. Ko yanzu ma da asirinsa ya tonu, an kamashi ne yana shirin kaiwa wani abokin huldarsa sassan jikin dan Adam ne. Me magana da yawun sojin, Lieutenant Colonel Olabisi Olalekan Ayeni, ya tabbatar da kamen inda yace sun mikashi hannun 'yansanda.