Saturday, December 20
Shadow

Duk Labarai

Ana rade-radin gwamnan jihar Naija yayi Murabus

Ana rade-radin gwamnan jihar Naija yayi Murabus

Duk Labarai
WATA SABUWA: Mataimakin Gwamnan Neja, Yakubu Garba, Zaiyi murabus Mataimakin Gwamnan jihar Neja, Yakubu Garba, zai yi murabus daga mukaminsa "kowane lokaci daga yanzu", majiyoyi da dama sun shaidawa jaridar DAILY NIGERIAN. A shirye-shiryen murabus din, majiyoyin sun ce mataimakin gwamnan da ke cikin rikici ya fara kwashe wasu kayansa daga Gidan gwamnati a karshen mako. Wasu majiyoyi sun tabbatar wa DAILY NIGERIAN cewa sun ga yadda aka yi ta komowar kadarorin mataimakin gwamnan daga gidan gwamnati tsakanin Asabar da Lahadi. Majiyar ta kara da cewa "Kamar yadda nake magana da ku, ya kwashe kayansa da yawa daga gidan gwamnati zuwa gidansa na kashin kansa. DAILY NIGERIAN ta tattaro cewa wasu sarakunan gargajiya a jihar sun ziyarce shi a daren ranar Lahadin da ta gabata domin lal...
Matasan da suka goyi bayan Buhari na kiran tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya fito takara a 2027

Matasan da suka goyi bayan Buhari na kiran tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya fito takara a 2027

Duk Labarai
Shugaban tsohuwar kungiyar goyon bayan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Dr. Jibril Mustapha, ya yi kiran tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya fito takarar shugaban kasa a shekarar 2027. A sanarwar da ya fitar a Legas, yace ya kamata tsohon shugaban kasar ya amsa kiraye-kirayen da ake masa domin shine Najeriya ke bukata a yanzu. Yace Najeriya a yanzu tana bukatar shugaban kasa wanda zai hada kan kasar kuma Tsohon shugaba Goodluck Jonathan na da wannan abun da ake bukata.
Hukumar Sojojin Najeriya ta yi bayani dalla-dalla abinda zai faru ga duk farar hular da aka kama yana saka kayan sojoji

Hukumar Sojojin Najeriya ta yi bayani dalla-dalla abinda zai faru ga duk farar hular da aka kama yana saka kayan sojoji

Duk Labarai
Hukumar sojojin Najeriya ta yi bayani dalla-dalla abinda zai faru ga duk farar hular da aka kama yana saka kayan sojojin Najeriya. Shugaban sashen kula da huldar sojojin da farar hula, Maj. Gen. Gold Chibuisi ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai. Yace abinda doka ta tanada shine duk wanda aka kama da kayan sojojin alhali ba soja bane shine sojojin su kamashi su kaishi wajan 'yansanda ba tare da duka ko cin zarafi ba. Yace duk sojan da aka kama yana cin zarafi ana hukuntashi. Yace dalilin da yasa ba'a barin wadanda ba sojoji ba su saka kayan sojoji shine mutane ba zasu tantance sojojin Gaskiya ba. Yace kuma masu aikata miyagun laifuka da dama na amfani da kayan sojojin wajan cutar da jama'a.
Kalli Bidiyo: Yanda wata kwaila tawa Abokiyarta zagin kare dangi saboda ta mata kwacen saurayi

Kalli Bidiyo: Yanda wata kwaila tawa Abokiyarta zagin kare dangi saboda ta mata kwacen saurayi

Duk Labarai
Wata kwaila ta dauki hankula bayan da tawa kawarta zagin kare dangi saboda ta mata kwacen saurayi. Bidiyon hirarsu ta WhatsApp ya yadu sosai a kafafen sada zumunta inda mutane da yawa ke ta mayar da martani. Saurara ku ji a kasa: https://www.tiktok.com/@apple.sadeeq/video/7497605055982374150?_t=ZM-8vtTBuA4oAI&_r=1 Wasu da yawa abin ya basu dariya.
Da Duminsa: A karshe dai, Sanata Natasha Akpoti ta baiwa Sanata Godswill Akpabio hakuri inda tace yanzu ta gane kurenta

Da Duminsa: A karshe dai, Sanata Natasha Akpoti ta baiwa Sanata Godswill Akpabio hakuri inda tace yanzu ta gane kurenta

Duk Labarai
Sanata Natasha Akpoti ta fito ta baiwa kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio hakuri kan zargin da ta masa na nemanta. Saidai ta nemi hakurinne ta hanyar zunde da shagube. A cikin wasikar data wallafa a shafinta na facebook. Sanata Natasha ta ce cikin habaici tana baiwa Sanata Akpabio Hakuri. Tace ta gano cewa nasarar dan majalisa a wani lokacin ba jajircewa da cacanta ce ke kawota ba amma biyayya ga bukatar wani. Tace kaiconta da bata gane cewa ba kin bashi hadin kai abu ne da baya daya daga cikin dokokin da aka zayyana a majalisar. Tace tana bayar da hakuri saboda girmama sanin aiki da hake hakkin mutanenta fiye da sharholiya a bayan fage. Tace yanzu ta gane kuskurenta dan ta ga sakamakon abinda ta aikata inda ta gamu da tsaiko da fushi da nuna isa, dan haka ya...
TIRƘASHI: Saboda masifa da sa ido irin na mutane sai da suka gano cewa Rarara kwance ya baiwa yayansa rigar da ya saka ranar bikinsa.

TIRƘASHI: Saboda masifa da sa ido irin na mutane sai da suka gano cewa Rarara kwance ya baiwa yayansa rigar da ya saka ranar bikinsa.

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} TIRƘASHI: Saboda masifa da sa ido irin na mutane sai da suka gano cewa Rarara kwance ya baiwa yayansa rigar da ya saka ranar bikinsa. Me za ku ce?
Karanta Jadawalin ‘yan siyasar da Aka dakatar da binciken da EFCC ke musu bayan da suka koma jam’iyyar APC

Karanta Jadawalin ‘yan siyasar da Aka dakatar da binciken da EFCC ke musu bayan da suka koma jam’iyyar APC

Duk Labarai
A kwanannan an yi ta gasar komawa jam'iyyar APC tsakanin 'yan majalisa da gwamnoni. Saidai akwai manyan masu laifi da ake zargin sun saci kudin Talakawa kuma har hukumar yaki da rashawa da cin hanci EFCC ta fara bincikensu. Amma tun da suka Koma APC ba'a kara jin labarin binciken da ake musu ba. Gasu kamar haka: Godswill Akpabio: Ana zarginsa da satar kudin jiharsa ta Akwa-Ibom yayin da yayi gwamna da suka kai Naira Biliyan N108.1. Kuma EFCC ta fara bincikensa. Amma duk da haka ba'a hukuntashi ba, tunda ya koma APC shiru kake ji. ORJI UZOR KALU Shima Kalu an kamashi inda aka zargeshi da cin kudin jihar Abia lokacin yana gwamnan jihar. Har an yanke masa hukunci amma kuma tun da ya koma APC shima shiru kake ji. STELLA ODUAH An zargeta da satar Naira Biliyan 5...
Ƴansanda sun ce sun kuɓutar da mutum 10 da aka sace a titin Funtua-Gusau

Ƴansanda sun ce sun kuɓutar da mutum 10 da aka sace a titin Funtua-Gusau

Duk Labarai
Rundunar ƴansandan Najeriya ta ce ta kuɓutar da mutum goma da ake zargin ƴanbindiga sun yi garkuwa da su a kan babban hanyar Funtua zuwa Gusau. Wata sanarwa da mai magana da yawun ƴansandan Najeriya, ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce an samu nasarar kuɓutar da mutanen ne bayan samun bayanan sirri kan ayyukan ƴan bindigar - inda suka kuma daƙile wani yunkurin garkuwa da mutane a kan hanyar ta Funtua-Gusau. Olumuyiwa ya ce ƴansandan shiyyar Faskari da ke jihar Katsina ne suka yi nasarar kuɓutar da mutanen goma, bayan artabu da masu garkuwan - abin da ya sa suka tsere da munanan raunuka. "Jami'an mu sun fafata da ƴanbindigar, abin da ya janyo wasu suka tsere da raunuka. Sakamakon haka muka yi nasarar ceto mutum goma, ciki har da direbobi biyu da kuma fasinjoji takwas. Ba su samu ...