Saturday, May 9
Shadow

Duk Labarai

YANZU-YANZU: Gwamna Bago Ya Sanya Dokar Ta Baci A Garin Minna Biyo Bayan Rikìçe-Ŕikicen Ta Ta’ďdançi

YANZU-YANZU: Gwamna Bago Ya Sanya Dokar Ta Baci A Garin Minna Biyo Bayan Rikìçe-Ŕikicen Ta Ta’ďdançi

Duk Labarai
Gwamnan jihar Neja, Umaru Mohammed Bago, ya sanya dokar taƙaita zairga-zirgar baburan haya daga karfe 6 na yamma zuwa 6 na safe a Minna babban birnin jihar sakamakon yawaitar rikicin 'yan daba a birnin. A cewar gwamnan, yanzu haka an takaita zirga-zirgar 'yan acaɓa da babura masu ƙafa uku a wannan tsakanin. Bago ya bayyana hakan ne yayin wani muhimmin taron tsaro da masu ruwa da tsaki suka yi da sarakunan gargajiya da shugabannin hukumomin tsaro a gidan gwamnati yau Talata. ''Babu wanda zai sake ɗaukar kowane irin nau'i makami a garin Minna. Ina bai wa jami'an tsaro umarni, duk mutumin da kuka gani da makami ku ɗauke shi a matsayin ɗanfashi da makami.'' in ji shi. Ya bayyana cewa sabon matakin na da nufin daƙile matsalolin tsaro da ke ƙara taɓarɓarewa a babban birnin jihar. ...
An yankewa matashi hukuncin kìsà saboda kàshè Kishiyar mahaifiyarsa me dauke da juna biyu da diyarta a Kano

An yankewa matashi hukuncin kìsà saboda kàshè Kishiyar mahaifiyarsa me dauke da juna biyu da diyarta a Kano

Duk Labarai
Babbar kotu a jihar Kano ta yankewa matashi me suna Sagir Rijiyar-Zaki dan kimanin shekaru 22 hukuncin kisa bayan samunsa da laifin kashe kishiyar mahaifiyarsa da diyarta. Sagir ya yi amfani da sukundireba ya cakawa kishiyar mahaifiyarsa me suna Rabiatu Sagir me kimanin shekaru 25 sannan ya shage diyarta, Munawwara me shekaru 8 itama ta mutu. A ranar April 22, 2025 ne Mai shari'a Amina Adamu-Aliyu ya ce an gabatar da gamsassun shaidu da suka tabbatar wanda ake zargi yayi kisan. Dan haka ya yankewa wanda ake zargin hukuncin kisa ta hanyar Rataya.
Wani abu me kama da Bam ya fashe a Kaduna, Mutane 2 sun mutu, 3 sun jikkata

Wani abu me kama da Bam ya fashe a Kaduna, Mutane 2 sun mutu, 3 sun jikkata

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wani abu me kama da bam ya fashe a unguwar Abakpa dake kusa da tsohuwar NDA a cikin garin Kaduna. Abin yayi sanadiyyar mutuwar yara biyu,daya sunansa Imam me shekaru 13 dayan kuma Narin me shekaru 6. Lamarin ya farune a ranar Talata, 22 ga watan Afrilu. Tuni jami'an tsaro suka kai dauki wajan. Zuwa yanzu dai ba'a tabbatar da meme ya fashe ba. Wani shaida yace yana cikin wanda ya ji fashewar abin inda ya fito dag ya ga meme sai ya ga Imam ya jikkata, yace kamin su kaishi Asibiti ya rasu. Hakanan lamarin yayi sanadiyyar jikkatar mutane 3.
ABIN A YABA: Malama Hajara Kenan Wacce Ta Gina Katafaren Sabon Masallaci A Unguwar Ndeshi Dake Karamar Hukumar Mokwa A Jihar Neja

ABIN A YABA: Malama Hajara Kenan Wacce Ta Gina Katafaren Sabon Masallaci A Unguwar Ndeshi Dake Karamar Hukumar Mokwa A Jihar Neja

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Malama Hajara Kenan Wacce Ta Gina Katafaren Sabon Masallaci A Unguwar Ndeshi Dake Karamar Hukumar Mokwa A Jihar Neja Wace fata za ku yi mata?
‘Yan Bìndìgà sun sakawa mutanen jihar Zamfara harajin Naira Miliyan 60 saboda sun baiwa sojoji bayanan sirri aka kai musu samame

‘Yan Bìndìgà sun sakawa mutanen jihar Zamfara harajin Naira Miliyan 60 saboda sun baiwa sojoji bayanan sirri aka kai musu samame

Duk Labarai
'Yan Bindiga a jihar Zamfara sun kakabawa kauyuka 12 harajin Naira Miliyan 60 saboda sunce mutanen wadannan kauyukan sun baiwa jami'an tsaro bayanan sirri da suka kai ga kai musu hari da tarwatsa su. Garuruwan da 'yan Bindigar suka sakawa wannan harajin sun hada da Koloma, Dan Hayin Zargado, Zargado, Dan Godabe, Sabuwar Tunga, Makini, Bubaka, Yelwa, Bahwada, Koda, Manya, da Kabusu. Mutanen kauyen sun bayyana cewa idan suka sake basu biya wannan haraji ba, 'yan Bindigar zasu afka musu da kisa da garkuwa da kona musu gidaje. Bakatsine ne ya bayyana hakan a shafinsa na X inda yace idan ba'a dauki mataki ba, komai na iya faruwa. Tsohon Kansilan Dankurmi, Hon. Iliyasu Salisu Dankurmi ma ya tabbatar da hakan a hirar da BBChausa ta yi dashi.
Dokar-ta-ɓaci: Magoya bayan Fubara na gudanar da gangamin maida shi kan kujerarsa

Dokar-ta-ɓaci: Magoya bayan Fubara na gudanar da gangamin maida shi kan kujerarsa

Duk Labarai
Daruruwan magoya bayan dakatatcen gwamnan jihar River Siminalayi Fubara ne suka fito zanga-zanga a yau Talata, su na masu kira da a mayar da shi kan kujerar sa ta gwamna. RFI ta rawaito cewa sun dai faro tattakin ne daga kan hanyar Aggrey, inda suke rike da alluna masu ɗauke da rubuce-rubucen cewa "muna tare da gwamna Sim Fubara", "muna buƙatar a maido mana da gwamnanmu da muka zaɓa", da dai sauransu. Wannan ce dai gangami na baya-bayan nan da magoya bayan gwamnan suka gudanar, tun bayan dakatar da shi da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya yi a ranar 18 ga watan daya gaba. A tattakin da su ke yi, sun riƙa rera wakoki da kade-kade da raye-raye tare da rera addu'o'in fatan a dawo da Fubara kan karagar sa ta mulkin jihar Rivers. Dakatarwar dai ta shafi mataimakiyarsa Ngozi Odu da...
An sanar da ranar da za a binne Fafaroma

An sanar da ranar da za a binne Fafaroma

Duk Labarai
An sanar da ranar da za a binne Fafaroma. Fadar Vatican ta tabbatar da cewa za a yi jana'izar marigayi, Fafaroma Francis da ƙarfe 8 na safe agogon GMT, a ranar Asabar mai zuwa. Hakan na zuwa ne yayin da fadar ta fitar da bidiyon da ke nuna mamacin kwance a cikin akwatin gawa, a cocin Casa Santa Marta da ke gidansa. Bidiyon ya nuna gawar Fafaroma sanye da jar doguwar riga da hularsa ta fafaroma da kuma carbi a hannunsa. A ranar Laraba ne za a mayar da gawar St Peter's Basilica, inda za a ajiye shi domin mutane su yi masa bankwana har zuwa ranar Asabar da za a binne shi. Fafaroma Francis ya mutu ne a ranar Litinin yana da shekaru 88 a duniya, sakamakon bugun zuciya.