Friday, December 5
Shadow

Duk Labarai

Hukumar Wutar lantarki ta Abuja zata yankewa hedikwatar Sojoji dana ‘yansanda wuta saboda bashi

Hukumar Wutar lantarki ta Abuja zata yankewa hedikwatar Sojoji dana ‘yansanda wuta saboda bashi

Siyasa
Hukumar wutar lantarki ta Abuja ta bayyana cewa, zata yankewa manyan ma'aikatu da yawa wuta saboda bashin kudin wutar da ake binsu. Ta bayyana cewa, daga cikin hukumin da ake bin bashin akwai hukumar sojojin, dana 'yansanda da ma'aikatar mata ta tarayya, da jihar Kogi, da ma'aikatar Ilimi, da ma'aikatar masana'antu. Hukumar tace ba wata ma'aikata da zata dagawa kafa zata yanke mata wuta. Hakan na kunshene a cikin sanarwar da hukumar wutar ta fitar.
Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya ce ya yi niyyar ɗaukar sojoji milyan ɗaya da ƴan sanda milyan ɗaya da a ce ya zama shugaban Najeriya a zaɓen 2023

Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya ce ya yi niyyar ɗaukar sojoji milyan ɗaya da ƴan sanda milyan ɗaya da a ce ya zama shugaban Najeriya a zaɓen 2023

Kano, Rabiu Musa Kwankwaso
Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya ce ya yi niyyar ɗaukar sojoji milyan ɗaya da ƴan sanda milyan ɗaya da a ce ya zama shugaban Najeriya a zaɓen 2023 Ɗan takarar shugaban ƙasar na jam'iyyar NNPP a zaɓén na 2023 da ya gabata, Engr Rabi'u Musa Kwankwaso ya furta hakan a hirarsa da BBC Hausa, ya ce wannan matakin zai inganta harkokin tsaron Najeriya da ya tabarbare a wasu sassan ƙasar. Wane fata zaku yi masa?
Mugunta ko cin Amana? Ji yanda shugaban wani kauye a jihar Katsina ya karbi cin hancin Naira dubu dari bakwai(700,000) ya amince aka kaiwa mutanen kauyensa hari har aka kash-she 30

Mugunta ko cin Amana? Ji yanda shugaban wani kauye a jihar Katsina ya karbi cin hancin Naira dubu dari bakwai(700,000) ya amince aka kaiwa mutanen kauyensa hari har aka kash-she 30

Katsina, Tsaro
Gwamnan Jihar Katsina, Dr. Umar Dikko Radda ya bayyana yanda wani shugaban kauye ya karbi Naira dubu dari bakwai ya amince aka kai hari akan kauyenshi wanda yayi sanadiyyar kisan mutane 30. Gwamnan yace an samu hakanne a Guga dake Bakori. Ya kara da cewa ba zasu kyale ko wanene aka samu da hannu a harkar 'yan Bindigar ba. Saboda rayuwar mutanen jihar tafi ta mutum daya ko wanene shi.
Kan mu ya daure, Bamu san wanne hukunci zamu yi amfani dashi ba>>Hukumar ‘yansandan jihar Kano bayan da aka aika mata hukunce-hukuncen kotu har 5 da suka shafi masarautar Kano, saidai ta bayyana abinda zata yi nan gaba

Kan mu ya daure, Bamu san wanne hukunci zamu yi amfani dashi ba>>Hukumar ‘yansandan jihar Kano bayan da aka aika mata hukunce-hukuncen kotu har 5 da suka shafi masarautar Kano, saidai ta bayyana abinda zata yi nan gaba

Kano, Siyasa
Hukumar 'yansandan jihar Kano ta bayyana tsaka mai wuya da take ciki kan hukunce-hukuncen kotu har guda biyar da aka yi kan masarautar Kano. Kwamishinan 'yansandan jihar, Mr Usaini Gumel ne ya bayyanawa manema labarai hakan inda yace sun tattara duka wadannan hukunce-hukuncen 5 sun aikewa da shugaban 'yansanda na kasa yayin da shi kuma ya aikawa da ministan shari'a. Yace suna jiran ministan shari'ar ya gaya musu da wane hukunci zasu yi amfani. Yace da zarar sun samu umarni daga ministan shari'ar, zasu zartas da hukuncin da doka ta amince dashi. Yayi kira kan kafafen yada labarai da su rika tantance labari kamin su yadashi.
An soki Peter Obi saboda kiran ‘yan Bindigar Arewa ‘yan Ta’dda amma yaki kiran ‘yan IPOB da ‘yan ta’adda

An soki Peter Obi saboda kiran ‘yan Bindigar Arewa ‘yan Ta’dda amma yaki kiran ‘yan IPOB da ‘yan ta’adda

Siyasa
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour party a zaben shekarar 2023, Peter Obi ya yi Allah wadai da harin da 'yan IPOB suka kai da ya kashe sojoji 5 a jihar Abia. A baya dai, an yi tsammanin ba zai yi magana akan lamarin ba saidai yazo yayi maganar. Amma kuma ya kaucewa kiran 'yan IPOB din da 'yan ta'adda. Tsohon hadimin Shugaban kasa Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad ne ya bayyana hakan inda ya dauko wani tsohon sakon na Peter Obi wanda yayi magana akan wani hari da aka kai jihar Filato inda ya kira maharan da sunan 'yan ta'adda. https://twitter.com/BashirAhmaad/status/1796877604475040183?t=ynvg3_I3Mpo8KjuxyO6U9w&s=19 A zamanin mulkin shugaban kasa, Muhammadu Buhari ne dai aka ayyana kungiyar ta IPOB dake ikirarin kafa kasar Biafra da sunan kungiyar ta'ddanci.
An kama yaro dan shekaru 13, da dan shekaru 18 da wani me shekaru 45 da yin Fyade a jihar Gombe

An kama yaro dan shekaru 13, da dan shekaru 18 da wani me shekaru 45 da yin Fyade a jihar Gombe

Tsaro
Jami'an 'yansanda a jihar Gombe sun kama wani karamin yaro dan shekaru 13 saboda yiwa yarinya me shekaru 8 fyade. Ya aikata laifinne a karamar hukumar Akko dake jihar ta Gombe. Hakanan an kama wani Usman Husseini dan shekaru 18 da kuma wani Mohammed Yaya shi kuma dan shekaru 45 da duka ake zargi da yin fyade a jihar. Kakakin 'yansandan jihar, ASP Buhari Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace yaron ya ja yarinyar zuwa wata hanya da ba kowa inda acanne ya zakke mata. Shi kuma Mohammed Yahya yawa yarinya me shekaru 10 fyadene a lokuta daban-daban inda wani lokacin yake bata Naira 100 wani lokacin kuma ya bata Naira 50. Shima ya fito ne daga Tumu karamar hukumar Akko. Yace ana bincike akan lamuran kuma za'a gurfanar da wadanda ake zargi a Kotu.
An bayyana sunayen sojojin da Kungiyar IPOB ta kashe

An bayyana sunayen sojojin da Kungiyar IPOB ta kashe

Tsaro
Hukumar Sojojin Najeriya ta bayyana sunayen sojoji 5 da ake zargin 'yan Kungiyar IPOB sun kashe. An kashe sojojinne a ranar Laraba a Obikabia dake jihar Abia. sunayen sojojin sune: • Sergeant Charles Ugochukwu (94NA/38/1467)• Sergeant Bala Abraham (03NA/53/1028)• Corporal Gideon Egwe(10NA/65/7085)• Corporal Ikpeama Ikechukwu (13NA/70/5483)• Corporal Augustine Emmanuel (13NA/70/6663) Hukumar sojojin Najeriya dai ta sha Alwashin daukar mataki me tsauri dan rama kisan sojojin nata.