Friday, December 5
Shadow

Duk Labarai

Labari Me Dadi:Zamu rabawa mutane Miliyan 75 kudade kyauta, tsarin Npower ya dawo>>Inji Gwamnatin Tinubu

Labari Me Dadi:Zamu rabawa mutane Miliyan 75 kudade kyauta, tsarin Npower ya dawo>>Inji Gwamnatin Tinubu

Siyasa
Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta bayyana dawo da tsarin tallafawa mutane wanda ta tsayar a watannin da suka gabata. Ministan kudi, Wale Edun ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a matsayin shiri na cika shekara daya da gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta yi. Tsarin dai wanda ya hada da ciyar da dalibai, da Npower, da baiwa mutane gajiyayyu kudin tallafi da tallafawa 'yan kasuwa da sauransu a yanzu ya dawo zai ci gaba da aiki. Ministan yace dama a baya an tsayar da tsare-tsarenne dan bincike da kuma kawar da matsalolin dake cikin tsarin kuma yanzu an kammala. A dambarwar da aka yi ta dakatar da tsarin, ta hada da dakatar da ministan jin kai Beta Edu wadda aka yi zargin ta aikata ba daidai ba. Saidai a yayin da yake maganar, Mi...
Mulkin Tinubu ya talauta masu kudi da yawa>>Inji Atiku

Mulkin Tinubu ya talauta masu kudi da yawa>>Inji Atiku

Duk Labarai
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar wanda kuma shine dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP a zaben da ya gabata na shekarar 2023 ya soki gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bayan da ta cika shekara guda da kafuwa. Atiku yace tsare-tsaren gwamnatin Tinubu ta jefa mafi yawan al'umma cikin halin wahala inda kuma ta talauta masu kudi. Atiku yace Najeriya bata aiki a karkashin Tinubu inda yace Tinubun ya kasa kawo canji da ci gaban da ya mutane alkawari. Yace matakan da Tinubu ya dauka sun ma kara jefa mutanene cikin halin kaka nikayi. Yace matsayin da tattalin arzikin Najeriya yake ciki a yanzu yafi muni idan aka kwatanta da shekara daya data gabata. Yace gwamnatin Tinubun ta karawa mutane wahala ne akan wahalar da ake ciki wadda gwamnatin tsohon s...
Sai an shekara 6 ana shan wahalar da cire Tallafin man fetur ya kawo>>Inji Shugaban ADC

Sai an shekara 6 ana shan wahalar da cire Tallafin man fetur ya kawo>>Inji Shugaban ADC

Siyasa
Shugaban jam'iyyar ADC, Dr Ralphs Okey Nwosu ya bayyana cewa, sai an shekara 6 ana wahala kamin a kawo karshen wahalar da cire tallafin man fetur ya jefa mutane. Ya bayyana hakane hirar da Daily Trust ta yi dashi. Cire tallafin man fetur ya jefa mutane da yawa a cikin matsin rayuwa inda mutane suka rika fama da abinda zasu ci wanda a baya ba haka bane. Saidai Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta bayyana cewa, wannan mataki ne data dauka dan amfanar al'umma baki daya wanda kuma na dolene.
Ba A Taɓa Gwamnatin Da Ta Kawo Wa Nijeriya Bàĺà’ì Da Mùśìbà Kamar Gwamnatin Buhari Ba, Cewar Attahiru Bafarawa

Ba A Taɓa Gwamnatin Da Ta Kawo Wa Nijeriya Bàĺà’ì Da Mùśìbà Kamar Gwamnatin Buhari Ba, Cewar Attahiru Bafarawa

Duk Labarai
Daga Imam Aliyu Indabawa Tsohon Gwamnan jihar Sokoto Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa ya yi Allah wadai da masu baiwa Buhari da gwamnatinsa kariya yana mai cewa duk mutumin da zai iya fitowa ya kare Buhari da gwamnatinsa to za su haɗu da shi a lahira a gaban Allah. A yayin tattaunawarsa da kamfanin watsa labarai na BBC Hausa tsohon gwamnan ya ce," Bala'in da Buhari ya kawo ƙasar nan na lalacewar damokraɗiya da cin hanci ni dai a rayuwata ban taba ganin gwamnatin da ta kawo mana bala'i da masifa kamar ta Buhari ba." Ya kuma nuna takaicinsa kan yadda gwamnatin Buhari ta ciyowa Nijeriya mummunan bashi na tiriliyoyi amma babu wani aiki da aka yi da kuɗin, ya ce wannan sai an je lahira za a yi shari'a a kansa.

Saboda yawan kudin da ya sata, Idan aka sakani wuta iri daya data Hadi Sirika ba’a min Adalci ba>>Inji Wannan mutumin

Duk Labarai
Wani mutum dan Najeriya ya bayyana cewa, idan aka sakashi wuta iri daya da ta tsohon ministan Sufurin Jiragen sama, Hadi Sirika ba'a masa adalci ba. Mutumin ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta kuma ya fadi dalilinsa na cewa Hadi Sirika ya saci kudi da yawa. Hadi Sirika dai na fuskantar tuhume-tuhume kan zargin satar Biliyoyin Naira da suka hada da biliyan 2 wanda ake zargin ya sata shi da diyarsa da surukinsa da kuma Biliyan 19 wadda ake zargin ya sata tare da kaninsa.
Hoto:Wannan mutumin ya mutu a dakin Otal bayan yin lalata da karuwa

Hoto:Wannan mutumin ya mutu a dakin Otal bayan yin lalata da karuwa

Duk Labarai
Wani mutum a kasar Afrika ta kudu ya mutu a dakin Otal bayan yin fasadi da karuwa. Matan dake gidan karuwan sun dakata da aiki bayan faruwar lamarin da ya girgizasu. Rahoton yace bayan da suka gama abinda zasu yi, karuwar ta taba mutumin inda ta ga ya mutu baya motsi. Anan ne aka kira jami'an tsaro dana lafiya inda suka tabbatar da cewa ya mutu. Ana bincike dan gano abinda yayi sanadiyyar mutuwarsa.
Kungiyar kwadago ta NLC ta ki amincewa da tayin Naira Dubu sittin(60,000) a matsayin mafi karancin Albashi, zata shiga yajin aiki

Kungiyar kwadago ta NLC ta ki amincewa da tayin Naira Dubu sittin(60,000) a matsayin mafi karancin Albashi, zata shiga yajin aiki

Siyasa
Kungiyar kwadago ta NLC ta ki amincewa da tayin Naira Dubu sittin(60,000) a matsayin mafi karancin Albashi. Wannan shine tayi na 4 da gwamnatin tarayya tawa NLC a cikin watanni 2 da aka shude ana tattaunawar. NLC dai ta sakko daga bukatar ta ta cewa sai an biya Naira 615,000 a matsayin mafi karancin albashi inda ta nemi yanzu a biya N118,000 zuwa N497,000. Wakilin NLC, Benson Upah ya bayyana cewa, Gwamnatin ba da gaske take ba da take cewa zata biyasu Naira Dubu sittin(60,000). Yace Gwamnatin ce ta jawo wannan matsala inda ta kawo tsare-tsare wanda suka saka al'umma cikin wahala
Kalli Abincin da ake baiwa Mahajjata a kasar Saudiyya: Mahajjatan sun koka inda suka ce duk da biyan Naira miliyan 8 a matsayi  kudin aikin hajjin bana abincin da ake basu kenan

Kalli Abincin da ake baiwa Mahajjata a kasar Saudiyya: Mahajjatan sun koka inda suka ce duk da biyan Naira miliyan 8 a matsayi kudin aikin hajjin bana abincin da ake basu kenan

Duk Labarai
Mahajjatan Najeriya a kasar Saudiyya sun koka da kalar abincin da ake basu duk da biyan Naira Miliyan 8 a matsayin kudin aikin hajjin bana. Daya daga cikin mahajjatan me suna Babagana Digima ne ya wallafa hoton kalar abincin da ake basu a shafinsa na facebook. Abincin dai koko ne da kosai guda 3. Babagana Digima ya kara da cewa, mahajjata yanzu sun koma bara dan neman abinda zasu ci saboda kudinsu dala $300 daya rage daga cikin dala $500 da suke da ita har yanzu ba'a basu ba. Hukumar Alhazai ta kasa, National Hajj Commission of Nigeria (Nahcon) da take martani akan lamarin, tace ta sa a yi bincike kan lamarin.
Kasar Japan zata gina Lifter wadda zata rika kai mutane sauran duniyoyi dake wajen Duniyar mu dan su ga yanda al’amura ke gudana

Kasar Japan zata gina Lifter wadda zata rika kai mutane sauran duniyoyi dake wajen Duniyar mu dan su ga yanda al’amura ke gudana

Duk Labarai
Wani kamfani na kasar Japan me suna Obayashi Corporation wanda shine ya gina gini mafi tsawo a kasar na shirin gina Lifter wadda zata rika kai mutane wajen Duniyar mu dan su ga yanda lamura ke gudana. Kamfanin yace zai fara wannan gini ne a shekara me zuwa watau 2025 wanda ake tsammanin kammalashi a shekarar 2050. Wannan lamari dai ya zowa mutane da mamaki amma wanda yace zai hadiye kota sai a sakar masa a gani.