Monday, April 27
Shadow

DSS ta sake kama dan Gwagwarmaya Mahadi Shehu

Hukumar ‘yansandan farin kaya ta DSS ta sake kama dan Gwagwarmaya Mahadi Shehu a Kaduna.

Rahoton Daily Trust yace an kama Mahadi Shehu ne a Unguwar Dosa da misalin karfe 11 na safe.

Saidai zuwa yanzu babu karin bayanin dalilin kamashi.

A watan Disambar da ya gabata ne dai aka kama Mahdi Shehu bisa zargin watsa labarin da ba daidai ba.

Na kusa dashi sun bayyana cewa suma basu san dalilin kamen ba.

Karanta Wannan  Tsohuwar Ministar Jin Kai, Betta Edu da aka sauke saboda zargin karkatar da kudin Talakawa ta samu kyautar girmamawa a jami'ar Calabar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *