Thursday, February 19
Shadow

Duk Labarai

Babu yarjejeniyar yin karɓa-karɓa tsakanina da Atiku – Kwankwaso

Babu yarjejeniyar yin karɓa-karɓa tsakanina da Atiku – Kwankwaso

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta raɗe-raɗin da ke cewa an cimma yarjejeniya tsakaninsa da tsofaffin ƴan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyun hamayyar ƙasar - Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP - kan cewa kowannensu zai yi mulki na wani wa'adi. A hirarsa da BBC, Kwankwaso ya ce bai san da maganar ba, amma ya samu labarin cewa ɓangaren Atikun na ta "yin taruka da shugabannin yankin ciki har da malamai, suna faɗa masu wannan magana".
Ni da ‘yan Najeriya muna cikin farin cikin gyara matatar mai ta Warri – Tinubu

Ni da ‘yan Najeriya muna cikin farin cikin gyara matatar mai ta Warri – Tinubu

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce "shi da 'yan ƙasar suna cike da farin ciki" sakamakon gyara matatar mai ta garin Warri da kamfanin mai na NNPCL ya yi. Wani saƙo da shugaban ya wallafa a shafinsa na X ya ce "hakan zai ƙara wa 'yan Najeriya ƙwarin gwiwa kan fatan da suke da shi game da alƙawuran da muka yi". Ya ƙara da cewa labarin "hanya ce mai kyau ta kammala shekarar 2024 idan aka ƙara da nasarar da aka samu kan matatar mai ta Fatakwal". Yayin wani taron manema labarai a yau Litinin, shugaabn kamfanin NNPCL Mele Kyari ya bayar da sanarwar cewa sun gyara matatar kuma ta ci gaba da aiki a matakin kashi 60 cikin 100 na ƙarfinta. A cewar Tinubu: "Tun da yanzu matatar Warri na aiki bisa kashi 60 cikin 100, tsarin gwamnatina na samar da tabbataccen makamashi yana kan hanya. "...
Zamu kawo Saukin Rayuwa>>Inji Gwamntin Tarayya

Zamu kawo Saukin Rayuwa>>Inji Gwamntin Tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bakin Ministan kudi da tattalin Arziki, Wale Edun ta bayyana cewa, zata kawo saukin rayuwa ga 'yan Najeriya ta hanyar saukaka farashin kayan abinci. Ya bayyana hakane bayan ganawa da shugaban kasar ranar Lahadi a Legas, yace gwamnatin zata samar da karin ayyukan yi a shekarar 2025 bayan samun saka hannun jari daga kasar Saudi Arabia Minista Edun bai dade da dawowa daga kasar Saudi Arabia ba biyo bayan ziyarar da Shugaba Tinubu ya kai kasar kan maganar zuba jari a Najeriya. Ministan ya bayyana cewa sun dawo da albishir daga kasar Saudi Arabia cewa za'a saki karin ayyuka a Najeriya. Yace Kasar Saudi Arabia ta kara jarin da take dashi a bangaren kiwon dabboni a kanfanin Olam da dala Biliyan $1.2 Ya kara da cewa kuma a yanzu ana rani ne, zasu tabbatar an s...
Hankula sun koma kan Shugaban kamfanin mai na kasa NNPCL yayin da saura kwanaki kalilan ya cika shekarun barin aiki

Hankula sun koma kan Shugaban kamfanin mai na kasa NNPCL yayin da saura kwanaki kalilan ya cika shekarun barin aiki

Duk Labarai
Shugaban kamfanin mai na kasa, NNPLC, Mele Kolo Kyari, saura kwanaki kalilan ya cika shekarun barin aiki watau 60. Nan da ranar 8 ga watan Janairu ne dai Mele Kolo Kyari zai cika shekaru 60 wanda a doka ya kamata ya sauka daga kan mukaminsa dan a nada wani shugaban kamfanin. Mele Kolo Kyari shine shugaban kamfanin NNPCL da yafi dadewa akan kujerar tun bayan da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya nadashi mukamin a ranar July 2019 inda a yanzu ya shafe shekaru sama da biyar akan kujerar kenan. Saidai inda gizo ke sakar shine Bayan da kamfanin NNPC ya koma na 'yan kasuwa ya fita daga hannun Gwamnati ya kuma canja suna zuwa NNPCL, doka ta baiwa Mele Kolo Kyari damar zai iya ci gaba da zama a matsayin shugaban kamfanin har nan da shekarar 2027. Wasu rahotanni kamar yanda jarid...
Mutanen dake zaune kusa da iyakar Najeriya da Nijar sun shiga fargaba biyo bayan sa in sar data barke tsakanin kasashen biyu

Mutanen dake zaune kusa da iyakar Najeriya da Nijar sun shiga fargaba biyo bayan sa in sar data barke tsakanin kasashen biyu

Duk Labarai
Wasu daga cikin mutanen dake zaune akan iyakokin Najeriya da Nijar sun shiga zullumi biyo bayan cece kucen da ya barke tsakanin kasashen biyu. Shugaban mulkin soji na Jamhuriyar Nijar, Brig Gen Abdourahmane Tchiani ya zargi cewa Najeriya ta girke sojojin kasar Faransa tare da kafa sansanin yiwa 'yan ta'adda atisaye. Saidai me baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu ya karyata wannan zargi inda yace Babu inda Najeriya ta kafa sansanin sojojin kasashen waje. Ribadu yace wannan kokari ne na kawar da hankalin mutane daga gazawar gwamnatin ta Jamhuriyar Nijar. Da yake bayyana rashin jin dadinsa kan lamarin, wani mazaunin jihar Sokoto, Muhammad Illiyasu ya rantse da Allah cewa, cikin shekaru 30 da yake rike da sarautar Magajin garin Balle a karamar hukumar G...
Saboda jin dadin Cire tallafin man fetur da Gwamnatin Tinubu ta yi da kakaba Haraji kala-kala akan ‘yan kasa, bankin Duniya ya baiwa Najeriya bashin Dala Biliyan $1.5

Saboda jin dadin Cire tallafin man fetur da Gwamnatin Tinubu ta yi da kakaba Haraji kala-kala akan ‘yan kasa, bankin Duniya ya baiwa Najeriya bashin Dala Biliyan $1.5

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, biyo bayan cire tallafin man fetur da kakaba haraji kala-kala akan 'yan Najeriya da Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta yi, bankin Duniya ya baiwa Najeriya bashin dala Biliyan $1.5. Cire tallafin man fetur da kakaba haraji, sharudane da bankin Duniyar ya gindayawa Najeriya wanda sai ta cikasu kamin ya bada bashin da ake nema. Bankin Duniyar da farko ya fara sakin dala Miliyan $750m a cikin watanni shida wanda masana suka ce shine mafi saurin lokaci da Najeriya ta samu bashi. Saidai sauran kudin bankin Duniyar yayi jan kafa wajan amincewa ya bayar dasu saboda Najeriya ta ki saurin kaddamar da fara karbar haraji. Sauran kudin dai a hankali za'a ci gaba da sakarwa Najeriya su bisa sharadin cika wasu sharudda da bankin Duniyar zai gindaya.
Cutar Prostate Cancer grade 3 ta kama Shugaban Israela Benjamin Netanyahu

Cutar Prostate Cancer grade 3 ta kama Shugaban Israela Benjamin Netanyahu

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Likitoci sun tabbatar da cutar Prostate Cancer grade 3 ta kama Firaiministan Israela, Benjamin Netanyahu. Hakan ya haifar masa da cutar yoyon Fitsari. Dalilin hakan ne yasa dole za'a yi masa tiyata. Hakan yasa aka dage shari'ar da ake shirin yi akansa a kotu ta zargin rashawa da cin hanci. Wasu dai na ganin cewa, wannan dabara ce da Benjamin Netanyahu yake yi an kawar da hankali akan Shari'ar tasa har maganar ta shirice. Hakanan ko da yakin da Benjamin Netanyahu ke ta dagewa ake yi da kungiyar Hamas, ana ganin kamar yana yin wannan dagiya ne saboda ya gujewa zarge-zargen rashawa da cin hanci da ake masa da kuma tsawaita ranar yin zabe.
Kalli Bidiyo: Wannan matashin ya raba gardama kan su wanene a gaba tsakanin yaran shago a Farm Center da Kwari

Kalli Bidiyo: Wannan matashin ya raba gardama kan su wanene a gaba tsakanin yaran shago a Farm Center da Kwari

Duk Labarai
Wani matashi da bidiyonsa ke ta yawo a shafukan sada zumunta ya dauki hankula bayan raba gardama da yayi tsakanin matasan Farm Center dana Kwari. Yace ya ziyarci wani abokinsa a Farm Center inda ya siyasa musu abincin dubu 3 kowannensu. kalli Bidiyon anan https://twitter.com/bapphah/status/1872882854084132903?t=ihZdF9d8gJOVb5acIaJlUQ&s=19 A bayaninsa yace, idan a Kwari ne yaron shago yayi haka ko ya yake saka kaya masu tsada, korarsa za'a yi a ce yanawa me gidansa sata. Masu Sharhi akan wannan bayani na wannan matashi da yawa dai wasu sun yadda dashi inda wasu suka karyatashi. Wasu kuwa sun ce Farm Center ta matasa ce inda ita kuma Kwari ta dattawa ce, shiyasa.