Monday, December 15
Shadow

Duk Labarai

Jirgin kasa dake jigila tsakanin Kaduna zuwa Abuja ya taka tare da kashe yara mata tagwaye a jihar Naija

Jirgin kasa dake jigila tsakanin Kaduna zuwa Abuja ya taka tare da kashe yara mata tagwaye a jihar Naija

Duk Labarai
Jirgin kasan daya taso daga Abuja zuwa Kaduna ya kashe kananan yaran wanda tagwayene mata a karamar hukumar Tafa. Lamarin ya farune da misalin karfe 10 na safe ranar Asabar, kamar yanda jaridar The Cable ta ruwaito. Yaran, Hassana and Hussaina Baro shekarar su daya da watanni 6. Kakakin 'yansandan jihar Naija, Wasiu Abiodun ya tabbatar da daruwar lamarin. Yace yaran suna wasa ne akan titin jirgin kasan kamin lamarin ya faru.
Hotuna:Sojojin kasar Nijar sun kama kasurgumin dan Bindigar nan, Kachalla Baleri

Hotuna:Sojojin kasar Nijar sun kama kasurgumin dan Bindigar nan, Kachalla Baleri

Tsaro
Sojojin kasar Nijar sun kama kasurgumin dan Bindiga, Kachalla Baleri. Masanin harkar tsaro, Zagazola Makama ne ya bayyana hakan inda yace an kamashine a Rouga Kowa Gwani. Baleri wanda dan Shinkafine ya addabi mutane a Zamfara, Sokoto da Maradi. Ya jagorancin kisan mutane da yawa da kuma garkuwa da mutane da yawa. Yana daya daga cikin na hannun damar Kachalla Bello Turji kuma shine mutum na 40 mafi hadari da sojojin Najeriya suke nema ruwa a jallo.
Hotuna: Matashi Ya Raba Litattafai Gudu Dubu Goma Kyauta Ga Dalibai Domin Taya Gwamna Abba Murna Cika Shekara Guda Akan Mulki

Hotuna: Matashi Ya Raba Litattafai Gudu Dubu Goma Kyauta Ga Dalibai Domin Taya Gwamna Abba Murna Cika Shekara Guda Akan Mulki

Duk Labarai
Matashi Ya Raba Litattafai Gudu Dubu Goma Kyauta Ga Dalibai Domin Taya Gwamna Abba Murna Cika Shekara Guda Akan Mulki Shugaban Gidauniyar Sharu Sarakin Kwankwasiyya free computer training, Hon. Sharu Saraki ya rabawa dalibai littafin kimanin dubu goma domin taya Mai girma Gwamnan Kano Eng. Abba Kabir Yusuf murnar cika shekara daya akan mulki. Sannan kuma gidauniyar ta sake daukar nauyin dalibai mata ilimin kwamfuta kyauta a gidaunyar dake kan titin Airport road kusa da gidan man Danmarna kwanar kotun No-Man's-land.
YANZU-YANZU: Ga sabon taken Najeriya da za a koma yin amfani dashi daga yau dinnan:

YANZU-YANZU: Ga sabon taken Najeriya da za a koma yin amfani dashi daga yau dinnan:

Siyasa
YANZU-YANZU: Ga sabon taken Najeriya da za a koma yin amfani dashi daga yau dinnan: Wanda ya rubuta - Lilian Jean Williams (1960) wanda yayi kidansa - Franca Benda Ga Sabon Taken National Anthem din Nigeria ⤵️ Nigeria, we hail thee,Our own dear native land,Though tribe and tongue may differ,In brotherhood, we stand,Nigerians all, and proud to serveOur sovereign Motherland. Our flag shall be a symbolThat truth and justice reign,In peace or battle honour’d,And this we count as gain,To hand on to our childrenA banner without stain. O God of all creation,Grant this our one request,Help us to build a nationWhere no man is oppressed,And so with peace and plentyNigeria may be blessed. Ku bayyana mana ra'ayinku kan wannan mataki da shugaban kasa ya dauka na canja taken Najeriya....
Gwamnatin tarayya ta janye zargin ta’addanci da takewa shugaban Miyetti Allah, Bodejo

Gwamnatin tarayya ta janye zargin ta’addanci da takewa shugaban Miyetti Allah, Bodejo

Tsaro
A ranar Laraba, Gwamnatin tarayya ta janye zarge-zarge 3 na ta'ddanci da takewa shugaban Kungiyar Miyetti Allah Kautal Hore, Bello Bodejo. Tun a watan Janairu ne dai sojoji ke tsare da Bodejo bisa wannan zargi inda suka ki bayar da belinsa. Saidai a ranar Laraba da Ministan Shari'a ya je gabatar da Zarge-Zargen da akewa Bodejo dan ci gaba da shari'a, sai ya ce gwamnati ta janye karar data shigar akanshi. Wannan lamari dai ya zowa mutane da mamaki ganin cewa a baya gwamnatin ko beli ta ki yadda ta bayar da Bodejon. Ana dai zargin Bidejo ne da kafa wata kungiyar Funali wadda ake zargin ta ta'ddanci ce da kuma basu makamai da sauran kayan aiki.
A shekarar 2023, na shirya mulkin Najeriya yanda ya kamata amma Tinubu bai shirya ba>>Atiku

A shekarar 2023, na shirya mulkin Najeriya yanda ya kamata amma Tinubu bai shirya ba>>Atiku

Duk Labarai
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar kuma dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP a shekarar 2023 ya bayyana cewa, ya shirya mulkin Najeriya amma Shugaban kasaz Bola Ahmad Tinubu bai shirya ba. Saidai Atiku yace amma Tinubu bai makara ba, zai iya daukar matakan da suka kamata wajan magance matsalolin kasarnan idan da gaske yake. Atiku ya bayyana hakane a sakon da ya fitar na cikar mulkin Bola Ahmad Tinubu shekara daya akan mulki. Ya kara da cewa, Tinubu da mukarrabansa basu san hanyar da zasu dauka ba wajan magance matsalolin Najeriya, suna canki cankane akan abinda suke tunanin zai iya yin aiki.