Wednesday, February 18
Shadow

Duk Labarai

Najeriya ta kashe Naira Tiriliyan 4.4 wajan biyan bashi

Najeriya ta kashe Naira Tiriliyan 4.4 wajan biyan bashi

Duk Labarai
Babban bankin Najeriya ya nuna cewa,Gwamnatin tarayya ta kashe Naira Triliyan 4.4 wajan biyan bashi a watanni 3 na biyu na wannan shekarar watau tsakanin watannin April, May da June. Jimullar kudaden da gwamnatin tarayya ta kashe a cikin wadannan watanni 3 Naira Tiriliyan 6.8 ne gaba daya wanda daga ciki ne aka cire Naira Tiriliyan 4.4 aka biyawa Najeriyar bashi watau dai Naira 2.4 ne suka yi saurawa gwamnati ta gudanar da sauran ayyukan kasa dasu. Hakan na nufin kaso 64.7 cikin 100 ne gwamnatin ta kashe wajan biyan bashi daga cikin kudaden shigarta. Hakan kuma na nufin Najeriya ta kashe fiye da abinda take samu a tsakanin wadannan watannin. Jimullar bashin da ake bin Najeriya dai ya kai Naira 121.67.
Atiku Abubakar ya taya Donald Trump murnar lashe zaben shugaban kasar Amurka

Atiku Abubakar ya taya Donald Trump murnar lashe zaben shugaban kasar Amurka

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya taya shugaban kasar Amurka, Donald Trump murnar lashe zaben shugaban kasar. A sakon da ya fitar ta shafinsa na sada zumunta, Atiku ya bayyana Tsarin Dimokradiyya a matsayin mafi dacewa duk da yana da matsalolinsa. Atiku ya kuma bayyana cewa irin gwagwarmayar da Donald Trump ya sha kamin ya zama shugaban kasar darasine babba da ya kamata a lura dashi. Hakanan Atiku ya kuma taya Donald Trump da mutanen kasar Amurka murnar nasarar zaben inda yace yana fatan Donald Trump din zai taimaka wajan aiwatar da zaben gaskiya a Najeriya da sauran kasashen Duniya.
Tinubu ya taya Donald Trump murna

Tinubu ya taya Donald Trump murna

Duk Labarai
Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya taya Donald Trump murna, inda ya ce a shirye yake su ci gaba da aiki tare domin inganta alaƙa tsakanin Najeriya da Amurka. Ya ce, "idan muka haɗa kai, za mu inganta tattalin arziki da zaman lafiya da magance matsalolin da al'umarmu ke fuskanta," kamar yadda mai taimaka masa kan harkokin watsa labarai, Bayo Onanuga ya sanar. Trump ne dai ya sanar da samun nasararsa a jawabinsa ga magoya bayansa, inda ya ce ya samu gagarumar nasara. Tinubu ya kuma yaba wa Amurkawa bisa yadda suka gudanar da zaɓen cikin lumana. Tinubu ya ce kasancewar Trump ya taɓa yin mulkin ƙasar, dawowarsa a matsayin shugaban ƙasar na 47 zai zo da gagarumar sauyi a tattalin arziki da ƙarin haɗin kai tsakanin Amurka da ƙasashen Afirka.
Yawan man fetur din da Najeriya take hakowa ya ragu

Yawan man fetur din da Najeriya take hakowa ya ragu

Duk Labarai
Bayanai daga babban bankin Najeriya sun nuna cewa yawan man fetur din da Najeriya ke hakowa ya ragu a watanni 3 na biyu na shekarar 2024. Man fetur din da Najeriya ke hakowa ya ragu da kaso 4.51% cikin 100 inda a yanzu Najeriya ke hako ganga Miliyan 1.27 a duk rana. A watanni 3 na farkon shekarar 2024 kuwa, Najeriya na hako ganga miliyan 1.33 ne wanda hakan ke nuna cewa an samu koma baya kenan. An dora alhakin hakan akan satar danyen man da kuma lalata bututun man fetur din wasu bata gari ke yi a yankin Naija Delta. Hakanan yawan man fetur din da Najeriyar ke hakowa yayi kasa da yawan wanda kungiyar kasashe masu arzikin man fetur OPEC ta bukaci kowace kasa ta rika hakowa watau Ganga Miliyan 1.58 a duk rana. Kamfanin man fetur na kasa, NNPCL dai ya sanar da cewa ya kashe Nair...
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya daga zaman majalisar zartaswa har sai abinda hali yayi saboda mutuwar shugaban sojojin kasa na Najeriya

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya daga zaman majalisar zartaswa har sai abinda hali yayi saboda mutuwar shugaban sojojin kasa na Najeriya

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya daga zaman majalisar zartaswa saboda mutuwar shugaban sojojin Najeriya Lt General Taoreed Lagbaja. Shugaban yace za'a sanar da sabuwar ranar yin zaman nan gaba. A yau, Larabane ya kamata a yi zaman na majalisar zartaswar amma aka dagashi sai abinda hali yayi saboda girmama shugaban sojojin da ya mutu. Shugaban ya kuma bayar da umarnin yin kasa-kasa sa tutocin Najeriya har nan da sati daya.
Ban san an kama kananan yara ba>>Gwamna Abba Kabir Yusuf

Ban san an kama kananan yara ba>>Gwamna Abba Kabir Yusuf

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayyana farin cikinsa da sakin kananan yara da aka kama bisa zargin cin amanar kasa. Gwamnan yace bai san an kama yaran ba sai bayan da aka kaisu gaban kotu a Abuja. Ya bayyana hakane a Asibitin Muhammadu Buhari Special Hospital inda aka kai yaran dan a dubasu a tabbatar suna cikin koshin lafiya. Gwamnan ya kuma godewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kan yafewa yaran inda yace zai tabbatar an sada su da iyalansu sannan a tabbatar sun koma makaranta dan Inganta rayuwarsu.
Donald Trump ya lashe zaben shugaban kasar Amurka

Donald Trump ya lashe zaben shugaban kasar Amurka

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Amurka na cewa Donald Trump ne ya lashe zaben shugaban kasar a karo na 2 inda ya doke abokiyar takararsa Kamala Harris. Tuni dai ya bayyana cewa dama an gaya masa ba a banza Allah ya tsallakar dashi daga yunkirin kisan da aka so yi masa ba. Shuwagabannin kasashe irin na faransa, Israela, Firaministan Ingila tuni suka taya Donald Trump murnar lashe zaben.
Da Duminsa: Shugaban Sojojin Najeriya ya mutu

Da Duminsa: Shugaban Sojojin Najeriya ya mutu

Duk Labarai
Kakakin shugaban kasa,Bayo Onanuga ya tabbatar da mutuwar shugaban sojojin kasa na Najeriya, Lt. General Taoreed Abiodun Lagbaja. Shugaban kasar ya bayyana cewa cikin takaici da alhini yana sanar da mutuwar shugaban sojojin kasa na Najeriya, Lt. General Taoreed Abiodun Lagbaja. Ya mutu ne yana da shekaru 56. Sanarwar tace ya mutu ne a daren ranar Talata a Legas bayan wata rashin lafiya. An haifeshi a shekarar February 28, 1968 kuma shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya nadashi Shugaban sojojin Najeriya ranar June 19, 2023.
Jihar Gombe ta kulla yarjejeniya da kamfanin kasar China dan samarwa da kanta wutar Lantarki

Jihar Gombe ta kulla yarjejeniya da kamfanin kasar China dan samarwa da kanta wutar Lantarki

Duk Labarai
Gwamnatin jihar Gombe ta samarwa da kanta hanyar samun wutar lantarki wadda ba sai ta dogara da gwamnatin tarayya ba. Gwamnatin ta sakawa wata yarjejeniyar samar da wutar me karfin megawatt 100 daga hasken Rana hannu tare da kamfanin China18th Engineering na kasar China. Gwamnan jihar Inuwa Yahya ya bayyana cewa, hakan zai basu damar karfafa huldar kasuwanci a jihar. Yace kudirin dokar da majalisa ta yi da ya baiwa jihohi damar samarwa da kansu wutar lantarki da rabata ne ya basu damar kaiwa ga wannan mataki.