Wednesday, February 18
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa:’Yansanda sun mamaye Otal din Azir da Azir Arena mallakin Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami dake tsare a hannun EFCC

Da Duminsa:’Yansanda sun mamaye Otal din Azir da Azir Arena mallakin Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami dake tsare a hannun EFCC

Duk Labarai
Rahotanni sun ce an ga 'yansanda sun mamaye Otal din Azir da Azir Arena dake jihar Sakkwato wanda mallakin tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami ne. Malami dai yana hannun hukumar EFCC tana bincikensa. Ana zarginsa da Almundahanar kudade masu yawa. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2002726485363470604?t=8ZQ3Nvma9rAUyTnPU9_1YA&s=19
Kalli Bidiyon: Na je wata makarantar Allo, nawa Malaminsu Albashin Naira dubu 50 duk wata>>Inji Peter Obi

Kalli Bidiyon: Na je wata makarantar Allo, nawa Malaminsu Albashin Naira dubu 50 duk wata>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa, na jam'iyyar Labour party a zaben shekarar 2023, Peter Obi ya bayyana cewa, ya je wasu makarantun Allo inda ya tambayi nawa ake biyan malaman? Yace Ya yiwa malaman Albashin Naira 50,000. Sannan kuma ya dauki malaman koyar da Turanci da Lissafi da kimiyya da fasaha suma ya musu Albashin Naira dubu 50,000. Ya bayyana cewa, yana da yakinin yaran zasu sama masu amfani anan gaba. https://twitter.com/dammiedammie35/status/2002659483143831905?t=jl551SBr27lgrN2dqstf6w&s=19
A’isha Buhari ta sake bayyana wani abin mamaki game da rayuwar Buhari da ya sa mutane rike baki

A’isha Buhari ta sake bayyana wani abin mamaki game da rayuwar Buhari da ya sa mutane rike baki

Duk Labarai
Matar tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Hajiya A'Isha Buhari ta bayyana cutar da tawa tsohon shugaban Katutu har ya rasu. Ta bayyana cewa, Shugaba Buhari yana fama da matsalar ciwon Sanyi. Tace kuma ciwon ya samo asali ne daga aikinsa na soja lokacin yana matashi, suna shiga daji, kaya na bushewa a jikinsa bayan sun jike. Sannan da sanyin AC, watau na'urar sanyaya daki ga kuma tsufa duk sun tarar masa a jiki. Hakanan ta kawo cewa, Tsohon shugaban ya sha taba lokacin yana matashi wanda hakan ma ya taimaka wajan rashin lafiyar tasa. Hajiya A'isha Buhari dai ta yi maganganu da yawa akan Marigayi Shugaba Buhari da suka baiwa mutane mamaki, wasu na ganin cewa bai kamata ta yi su ba.
Kalli Bidiyon:Matar Aure me ciki ta dauki hankula bayan data ce mijinta ya je ya roko mata shinkafar da aka dafa a makwabta tana son ci amma yaki

Kalli Bidiyon:Matar Aure me ciki ta dauki hankula bayan data ce mijinta ya je ya roko mata shinkafar da aka dafa a makwabta tana son ci amma yaki

Duk Labarai
Wata matar aure me ciki ta dauki hankula bayan data nemi mijinta ya je makwabta ya roko mata shinkafa da fa duka da suka dafa. An ga matar rike da kwano a wani Bidiyo da ya watsu sosai inda tacewa mijin nata ya shiga Makwabta ya roko mata shinkafar saboda tana son ci. Saidai mijin yaki, yace ta je da kanta ta roko da kanta. Ya nuna Tuwon da ya dafa a gidan inda yace me yasa ba zata ci ba? Lamarin dai ya jawo muhawara me zafi. https://twitter.com/metronaija/status/2002362363098325136?t=VHnTN94rnQQJgXJ5ptEFDg&s=19
Da Duminsa: Bayan da wannan sabuwar motar Alfarma ta Gwamnan Katsina ta Dauki hankula, Sarkin Mota ya bayyana ainahin farashin motar

Da Duminsa: Bayan da wannan sabuwar motar Alfarma ta Gwamnan Katsina ta Dauki hankula, Sarkin Mota ya bayyana ainahin farashin motar

Duk Labarai
Sabuwar motar gwamnan jihar Katsina, Umar Dikko Radda ta dauki hankula a kafafen sada zumunta inda ake ta maganarta. A yayin da ake ta hasashe akan farashin motar. Sarkin Mota ya bayyana farashin motar na gaskiya. Yace farashin motar Naira Miliyan 300 ne. Kuma yace kyauta aka baiwa gwamnan Katsinan Motar ba saye yayi ba. https://twitter.com/SarkinMota_AMF/status/2002559586709143977?t=EuDlE6Uuw47xhNxo6NUC3g&s=19
Da Duminsa: Hukumar NAFDAC ta yi gargadi kan cin Taliyar Indomie Vegetable Flavour noodles

Da Duminsa: Hukumar NAFDAC ta yi gargadi kan cin Taliyar Indomie Vegetable Flavour noodles

Duk Labarai
Hukumar kula da abinci da magunguna ta kasa, NAFDAC ta gargadi mutane akan kada su sayi Taliyar Indomie Vegetable Flavour noodles. Dalili kuwa shine an gano wani sinadari a cikinta da ka iya yiwa Lafiyar Mutane illa. Kamfanin Taliyar, ya bayar da umarnin 'yan kasuwa da suka sayeta su mayar da ita zuwa wajansu. Kamfanin dake yin taliyar,  Rappel Conso of France ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar. Hukumar NAFDAC tace an gano sinadarin ne bayan kai taliyar dakin bincike.
Kalli Bidiyon yanda Gwamna Dikko Radda na jihar Katsina yayi Subutar baki ya kira shugaba Tinubu da Marigayi a wajan taro

Kalli Bidiyon yanda Gwamna Dikko Radda na jihar Katsina yayi Subutar baki ya kira shugaba Tinubu da Marigayi a wajan taro

Duk Labarai
Wani Bidiyo ya bayyana inda aka ga Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda yayi Subul da baka ya kira Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da Marigayi a wajan taro. Yana kokarin yin maganane a kan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari. Saidai yayi sauri ya gyara. https://twitter.com/Pharmacio001/status/2002252205244481957?t=YzEM95qX7SBMpD-0AiQyrA&s=19