Saturday, June 27
Shadow

Da Duminsa: Ganduje da Doguwa sun bayyana wanda suke son a baiwa mataimakin gwamnan jihar Kano

Dan majalisar Wakilai, Alhassan Ado Doguwa da Tsohon shugaban jam’iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje sun bayyana wanda suke so a baiwa Mataimakin Gwamnan jihar Kano.

Duka su biyun sun bayyana Murtala Garo a matsayin wanda suke son a baiwa mataimakin Gwamnan jihar ta Kano.

Doguwa ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

Rahoton yace an cimma matsayar a zabi garo a matsayin mataimakin Gwamnan jihar Kano ne bayan wani zama da masu fada aji na jam’iyyar APC a jihar Kano suka yi ranar Asabar.

Kuma kaso 90 cikin 100 na mutanen suka ce sun amince a zabi Garo a matsayin mataimakin gwamnan jihar.

Karanta Wannan  Hedikwatar Tsaro Ta Kasa Ta Yi Wa Babban Soja MS Adamu Gayyatar Gaggawa Domin Ya Zo Ya Yi Bayanin Dalilinsa Na Azabtar Da Soja Abbas Har Na Tsawon Shekaru Shida

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *