Sunday, March 23
Shadow

Dansandan Najeriya ya manto Bìndìgàrsà a gidan giya bayan da yayi mankas

Rahotanni daga jihar Osun na cewa, Wani Dansanda ya manto Bindigarsa a gidan giya a jihar bayan da yayi Mankas da giya.

Rahoton yace lamarin ya farune a Osogbo babban birnin jihar ta osun.

An bayyana sunan dansandan da wannan lamari ya faru dashi da sunan Inspector Monday.

Saidai yayi karyar cewa ya mayar da Bindigar wajan da suke ajiye makamai, saidai da aka bincika an gano karya yake.

Hakan na zuwane yayin da ake tuhumar manyan ‘yansandan Najeriya kan batan Bindigu da yawa.

Karanta Wannan  A 2027 'yan Najeriya APC zasu zaba daga sama har kasa>>Inji Gwamnan Kaduna, Uba Sani

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *