Friday, February 7
Shadow

Gwamnati na da arzikin da za ta ɗauki nauyin tafiye-tafiyen Tinubu ko mai yawan su – Minista

Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce Najeriya na da arzikin da za ta iya daukar nauyin tafiye-tafiyen da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke yawan yi zuwa kasashen waje tun bayan hawansa mulki.

Tafiye-tafiyen da Tinubu ke yi zuwa kasashen waje na shan suka daga al’ummar ƙasar duba da matsalar tattalin arziki da ake fama da ita.

Sai dai da ya ke magana a shirin ‘Politics Today’ na Channels TV, Tuggar ya ce Tinubu, sabanin korafe-korafen da ake yi, har ma yana bukatar kara tafiye-tafiyen saboda mahimmancin dabarunsa da kuma amfanin da su ke da shi ga kasar.

Ministan ya bayyana cewa, Tinubu zai iya karfafa alaka da sauran shugabannin kasashen duniya ne kawai a yunkurinsa na dora kasar nan kan turba mai kyau ta hanyar yin tattaki zuwa ƙasashen..

Karanta Wannan  Hotuna: YANZU-YANZU Zanga-Zanga Ta Barke A Masarautar Rano Dake Kano Kan Rikicin Sarauta

Ya ce, “Wannan korafe-korafen ba su da tushe. Gwamnatin nan har yanzu sabuwa ce saboda an rantsar da shugaban kasa a shekarar 2023. Ta fuskar diflomasiya, har yanzu shi ne sabon shugaban kasa. Yana buƙatar yin hulɗa da abokan aikinsa da shugabannin ƙasashe don samun damar kulla dangantaka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *