Monday, August 10
Shadow

Gwamnonin Arewa sun bukaci gwamnatin tarayya ta saki kananan yara da aka kama ake zargi da cin amanar kasa

Gwamnan jihar Kano dana Bauchi da kungiyar Dattawan Arewa ta ACF sun nemi gwamnatin tarayya ta saki kananan yara da ake zargi da cin amanar kasa.

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf tuni ya baiwa babban lauyan jihar umarnin daukar mataki akan lamarin.

Hakanan kuma A bangaren gwamnan jihar Bauchi shime ya bayyana takaici da abinda ya faru.

Suma bangaren dattawan Arewa na ACF sun nemi gwamnati data saki yaran da gaggawa sannan kuma ta yi bincike kan tsaresu da aka yi ba bisa ka’ida ba.

Karanta Wannan  Ji yanda dan shekara 22 ya auri 'yar shekaru 16 a Kano bada sanin iyayensu ba amma Hisbah ta warware aure

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *