HASBUNALLAHU WA NI’IMAL WAKIL: Bèĺlò Țùŕjì Ya Kori Mutàñèn Gàriñ Bafàrawa.

Daga Datti Assalafiý
Shugaban barayin daji Be||0 Turj! ya kori mutanen dake zama a garin Bafarawa, kusan gaba daya mutanen garin sun watse zuwa neman mafaka a halin da ake ciki
Sannan Be||0 Turj! ya aika takarda zuwa ga mutanen garuruwan Kamarawa, Arume da Kagara, ya ce baya son ganin wani mutum a cikin garuruwan daga yau Lahadi zuwa misalin karfe 4 na yammaci
Akwai labarin da na gani, ance a daren jiya kadai kusan garuruwa 5 barayin daji suka yiwa hari a tsakanin jihar Katsina da Zamfara
Sannan jiya ‘yan bindiga sun kai harin ta’addanci makarantar Sakandare (GSS) dake garin Raka a karamar hukumar Tsafe jihar Zamfara inda suka kashe Malami sannan sukayi garkuwa da mutane da yawa
Abubuwan da suke faruwa a yankin Arewa na matsalar tsaro kamar babu Gwamnati a Nigeria, shin menene manufar da ta sa a yanzu Be||o Turj! yake ta tashin mutane da garuruwansu?
Ana ta zargin cewa duk garin da aka tasa a yankunan da ake fama da matsalar nan to akwai ma’adinan karkashin kasa masu daraja a garin, idan aka tada mutanen gari watakila Kasar Faransa zata mamaye gurin ta cigaba da mining kenan???
Kuma idan kun lura, ba’a so a kawar da Be||o Turj! ne, domin ba shakka akwai manyan azzalumai maciya amana da suke amfana da ta’addancinsa
Mu hadu mu kai karansu gurin Allah, duk wanda yake da hannu a wannan matsala Allah Ka dauki rayuwarsa