Tuesday, November 18
Shadow

Hukumar kula da birnin tarayya Abuja zata sake gina sabuwar Hukumar zabe me zaman kanta INEC, ‘yan Najeriya da yawa sun ce wata hanyar bata kudi ce

Hukumar kula da babban birnin tarayya Abuja, FCTA ta sanar da shirin sake gina sabuwar Hukumar zabe me zaman kanta, INEC.

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ne zai kaddamar da fara ginin na INEC wanda na daga cikin bikin cikarsa shekara 2 akan mulki.

Ba dai a bayyana ainahin nawaye kudin da za’a yi amfani dasu wajan sake gina sabuwar hukumar INEC din ba amma an ce zasu kai Biliyoyin Naira.

Da aka binciki cewa, me yasa FCTA zata gina INEC saboda lura da INEC hukuma ce me zaman kanta, wata majiya daga hukumar ta FCTA tace ai sune suka gina hukumomi da yawa a Abuja hadda ma majalisar tarayya.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Rawar da Tauraruwar fina-finan Hausa, Hannatu Bashir ta yi ta jawo cece-kuce sosai inda wasu ke cewa ba girman ta bane

Sannan sake ginin bashi da wata alaka da kokarin nuna iko da hukumar ta INEC.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *