
A daren jiya, an samu barin wuta sosai a babban birnin Niamey dake kasar Nijar.
An ga yanda makamai ke harba abubuwa sama.
A wani Bidiyo daya watsu sosai a kafafen sada zumunta, an ji mutane nata salati da hailala.
Wasu rahotanni sun ce wani abune aka gani yana shawagi a sararin samaniyar kasar wanda ba’a san dashi ba.
A filin jirgin kasar ma, an ga yanda mutane suka kidime kowa nata kansa.