
Hukumar EFCC a jihar Kano ta kama tsohon ɗan majalisar tarayya Hon. Muhammad Gudaji Kazaure bayan ta gayyaceshi ofishinta kuma ya kai kansa amma daga bisani ta naɗeshi zuwa Abuja.
Bayanan da Zuma Times Hausa ta samu sun ce, EFCCin tana neman bayanan wasu kyaututtukan kudade naira miliyan 14 da suka shiga asusun bankin tsohon dan majalisar a wani lokaci a shekarar 2019.
Me zaku ce?