Ka Yi Watsi Da Masu Suka, Ka Cigaba Da Ayyukan Cigaban Da Kake Yi, Sakon Tinubu Ga Wike.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bukaci Ministan Abuja, Nyesom Wike, da ya ci gaba da aikinsa na alheri ba tare da sauraron masu suka ba.
Tinubu ya bayyana hakan ne yau yayin kaddamar da sabun Dakin Taro na Ƙasa da Kasa da aka gyara kuma aka sake sanya mata suna Bola Ahmed Tinubu International Conference Centre a Abuja.