
Daliban Marigayi, Dr. Idris Dutsen Tanshi sun fito sun nesanta kansu da Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah inda suka ce ba dalibin malaminsu bane.
Sannan sun ce abinda yake yadawa a kafafen sada zumunta da kuma zama da ya kanyi da matan da ba nasa ba wai da sunan wa’azi, ba koyarwar Dr. Idris bace.
A baya dai an ga Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah tare da malama Juwairiyya zaune a kujera daya kusa da juna inda Bidiyon ya jawo cece-kuce sosai.
Hakanan a kwanannan ya wallafa Bidiyon tare da wata a kusa dashi tana karatun Qur’ani wanda shima ya jawo cece-kuce wasu na cewa matarsa ce wasu na cewa kanwarsa ce.
Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah dai yakan kawo labaran wasu abubuwan ban mamaki da yakance an kawo masa tambaya akai wanda sukan jawo cece-kuce.