
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya baiwa matar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu watau Remi Tinubu hakuri kan abinda matan jihar Rivers suka mata.
A jiya Juma’a ne dai hutudole ya kawo muku rahoton cewa, matan jihar ta Rivers ana tsaka da taro sun tashi sun tafi yayin da matar shugaban kasar ke tsaka da jawabi inda suka ce basa son saurarenta.
Wike ta bakin kakakinsa, Lere Olayinka ya bayyana cewa wannan abin kunyane kuma daukar nauyin matan aka yi.
Yace wanda ke cewa yana neman sulhu ne wai yake irin wannan abin inda yace ba da gaske yake ba.
Wike yace a madadin al’ummar jihar Rivers kuma a matsayinsa na dattijo daga jihar Rivers yana baiwa matar shugaban kasar Hakuri.