Tuesday, May 19
Shadow

Matan Yarbawa sun yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu Alkawarin samar masa da kuri’u Miliyan 1

Wata Kungiyar matan yarbawa a jihar Osun ta yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu Alkawarin kuri’u Miliyan 1 a zaben 2027.

Kungiyar tace shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ne zabinta a zaben 2027.

Matan ta bakin wakiliyarsu a jihar Osun, Adesola Ayangbil sun bayyana cewa, sun fara yakin neman zabe ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu gida’gida kamin zuwa zaben shekarar 2027.

Sun bayyana hakane a ofishin yakin neman zaben Tinubu da Shettima.

Sun ce sun yaba da shugabancin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a shekaru 2 da suka gabata.

Karanta Wannan  Matar Gwamnan jihar Borno ta karrama ma'aikataciya me daukar albashin Naira 30,000 data mayar da Naira Miliyan 4.8 da aka tura mata bisa kuskure kyautar Naira miliyan 1

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *