Friday, February 20
Shadow
Kalli Bidiyon: Ganin Me Bakin Kiyss a cikin Jirgin sama ya jawo cece-kuce

Kalli Bidiyon: Ganin Me Bakin Kiyss a cikin Jirgin sama ya jawo cece-kuce

Duk Labarai
Ganin Tauraruwar Tiktok me Bakin Kiss a cikin jirgin sama ya jawo cece-kuce sosai. Wasu dai sun yi mamaki inda da yawa ke cewa rakiya taje. Da yawa dai basu yi tsammanin ganinta a cikin jirgin saman ba. https://www.tiktok.com/@mebakinkiss4/video/7580358140101725458?_r=1&_t=ZS-91zemoBcOMD https://www.tiktok.com/@mebakinkiss4/video/7580396240706309384?_t=ZS-91zdrlwJQyu&_r=1
Kalli Bidiyon: Na kan ji Ba dadi idan naga Masu kudi na sayen motoci da jiragen sama na Miliyoyin Naira saboda da Kamfanoni suka bude da kudaden da Dukiyarsu ta habaka kuma sun samarwa mutane ayyukan yi>>Inji Dangote

Kalli Bidiyon: Na kan ji Ba dadi idan naga Masu kudi na sayen motoci da jiragen sama na Miliyoyin Naira saboda da Kamfanoni suka bude da kudaden da Dukiyarsu ta habaka kuma sun samarwa mutane ayyukan yi>>Inji Dangote

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Alhaji Aliko Dangote ya bayyana cewa akwai ban haushi sosai yanda wasu mas kudi ke kashe Miliyoyin kudade wajan sayen motocin Alfarma da jiragen sama. Yace wani lokacin idan yayi tafiya da jirginsa, babu ma wajan da zai ajiyeshi saboda duk filin jirgin an cikeshi da jiragen mutane. Yace maimakon wannan barnar kudin, kamata yayi ace masu kudin sun bude kamfanoni ne ta yanda Dukiyarsu zata habaka kuma su samarwa matasa ayyukan yi. https://www.tiktok.com/@soartvs/video/7580508561025846536?_t=ZS-91zVMhrvcLw&_r=1
Gfresh ya karo wulaqanci: Kalli Bidiyon yanda ya Sùmbàcì Amaryarsa da aka Daura musu aure jiya

Gfresh ya karo wulaqanci: Kalli Bidiyon yanda ya Sùmbàcì Amaryarsa da aka Daura musu aure jiya

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin kenan a wannan Bidiyon inda ya sumbaci Amaryarsa, Maryam da aka daura musu aure jiya. A jiya ne dai aka daura auren a garin Gombe kamar yanda Hutudole ya kawo muku. Abokinsa Aminu J. Town da sauransu ne suka shige gaba-gaba wajan wannan bikin. https://www.tiktok.com/@ib.exclusive/video/7580650872405871892?_t=ZS-91zUDDsqdCj&_r=1
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Ji labarin yanda ake zargin wani malami da yiwa yàrà 9 Lìywàdhì a Abuja

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Ji labarin yanda ake zargin wani malami da yiwa yàrà 9 Lìywàdhì a Abuja

Duk Labarai
Wasu iyaye na zargin wani malami da yiwa 'ya'yansu 9 Luwadi a Abuja. Lamarin kamar yanda gidan Rediyo da TV na Brekete Family suka ruwaito ya farune a Abuja inda iyayen har sun kai korafi wajan 'yansanda kuma har an kama wanda ake zargi. Saidai sun ce daga baya sun samu Rahoton cewa an sakeshi. Mutumin an ce har jan Sallah yana yi a unguwarsu sannan kuma yaran sun ce idan yayi Luwadi dasu yakan musu barazanar Mutuwa idan suka gayawa wani. https://www.tiktok.com/@sahabi_jaafar_yellow/video/7580518215625788693?_t=ZS-91zOVlLTp8D&_r=1
Fàdà ya dawo danye, Yanzu ne zan fito in maka tonon Silili in gayawa Duniya yanda kaso aikata Alfasha dani>>Sanata Natasha Akpoti ta gayawa Sanata Godswill Akpabio

Fàdà ya dawo danye, Yanzu ne zan fito in maka tonon Silili in gayawa Duniya yanda kaso aikata Alfasha dani>>Sanata Natasha Akpoti ta gayawa Sanata Godswill Akpabio

Duk Labarai
Sanata Natasha Akpoti ta ce dama irin damar da take son samu kenan wadda bata samu a bayaba ta tonawa sanata Godswill Akpabio asiri kan yanda ya nemi yin lalata da ita. Ta bayyana hakane bayan da sanata Godswill Akpabio ya maka ta a kotu yana neman ta biyashi diyyar Naira Biliyan 200 saboda zargin ta bata masa suna da zargin karya data masa na cewa ya so yin lalata da ita. Sanata Natasha Akpoti tace lallai ta samu sammacen kotu akan karar da Sanata Godswill Akpabio ya shigar akanta. Tace yanzu ne ta samu damar tona masa Asiri. A tace a baya abinda yasa bata tona masa asiri ba, a dokar majalisa sai ta gabatar da korafinta a gaban kwamitin bincike kamin taje kotu amma ba'a bata wannan damar ba amma yanzu ta ji dadi tunda da kansa ya kai magana kotu.
Bana cikin masu daukar nauyin tà’àddàncy a Najeriya>>Abubakar Malami

Bana cikin masu daukar nauyin tà’àddàncy a Najeriya>>Abubakar Malami

Duk Labarai
Tsohon Ministan shari'a a zamanin Mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Abubakar Malami ya bayyana cewa baya cikin masu daukar nauyin taaddaci a Najeriya. Ya bayyana hakane a matsayin martani kan wani rahoto da ya zargeshi da wasu manyan Arewa da alaka da wasu da ake zargin masu daukar nauyin ta'addanci ne. Malami yace a tarihinsa ba'a taba zarginsa ba ko aka kamashi ko aka masa shari'a akan daukar nauyin ta'addanci ba. Yace ko tsohon Janar din da ya bayar da labarin ba yace yana zarginsu bane, yace an gano suna da alaka ne da mutanen da ake bincike. Yace dan haka bashi da hannu a lamarin daukar nauyin ta'addanci a Najeriya.