Saturday, December 13
Shadow
Kwana daya bayan samun Rahoton cewa, zai fito takarar shugaban kasa, Gwamnatin Tarayya ta fara sukar Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan

Kwana daya bayan samun Rahoton cewa, zai fito takarar shugaban kasa, Gwamnatin Tarayya ta fara sukar Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan

Duk Labarai
Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan na da ‘yancin tsayawa takarar shugabancin ƙasar a shekarar 2027. Sai dai ta jaddada cewa ‘yan Najeriya ne za su yi masa hukunci saboda ba su manta 'munin' mulkin Jonathan ba, ta kuma kwatanta mulkin Tinubu da abin da ta bayyana a matsayin “gagarumin ci gaban tattalin arziƙi” Fadar shugaban ƙasar ta kuma ɗora alhakin fara yaƙin neman zaɓe da wuri kan masu neman kifar da shugaba mai ci. Hakan na zuwa ne a rana guda da jam’iyyar PDP ta bayyana cewa ba za ta bai wa Jonathan tikitin tsayawa takara kai tsaye ba, inda ta bayyana shi a matsayin ɗaya daga cikin “zaɓuɓɓukan da take dubawa.
Kalli Bidiyon: Kalaman da Sheikh Lawal Triumph ya fadi akan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Sam basu dace ba, kuma nasan zaku ce ni dan fim ne be kamata in saka baki ba, to Ku sani Annabu aka taba>>Inji Bosho

Kalli Bidiyon: Kalaman da Sheikh Lawal Triumph ya fadi akan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Sam basu dace ba, kuma nasan zaku ce ni dan fim ne be kamata in saka baki ba, to Ku sani Annabu aka taba>>Inji Bosho

Duk Labarai
Tauraron Fina-finan Hausa a bangaren Barkwanci, Bosho ya yi martani kan zargin da akewa malam Lawal Triumph kan yin kalamai da basu dace ba ga Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Bosho yace kalaman da Malam Lawal Triumph yayi amfani dasu basu dace ba. Bosho Yace yasan wasu zasu ce a matsayinsa na dan Fim kada ya saka baki amma yace duk wanda ya taba Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ko wanene ba zasu bari ba. https://www.tiktok.com/@dr.ishakayahaya/video/7555296755907185928?_t=ZS-909mkB72drV&_r=1
Cikar Najeriya shekara 65 da samun ‘Yanci: Gwamnatin Najeriya ta bayar da hutu ranar Laraba

Cikar Najeriya shekara 65 da samun ‘Yanci: Gwamnatin Najeriya ta bayar da hutu ranar Laraba

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta sanar da gobe Laraba a matsayin ranar hutu a ƙasar somin bikin cikar ƙasar shekara 65 da samun ƴancin kai. Cikin wata sanarwa da ministan cikin gida na ƙasar, Olibunmi Tunji-Oja ya fitar, ya taya ƴan Najeriya murnar cimma wannan ''babban matsayi''. Ministan ya kuma buƙaci ƴanƙasar su ci gaba da nuna kishin ƙasa da hadin kai da juriya, waɗanda ya ce su ne ke taimaka wa ƙasar wajen dunƙulewa tun lokacin samun ƴancin kai a 1960. A ranar 1 ga watan Otoban 1960 ne dai Najeriya ta samun ƴancin kai daga Turawan mulkin Birtaniya da suka yi mata mulkin mallaka.
Kalli Bidiyo: Sheikh Musa Asadussunnah yace kamar yanda ake shirin Titsiye, Malam Lawal Triumph a hada da Malam Nazifi Alkarmawi saboda yace idan mutum yayi mafarki ya ga Raqumi, Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya gani

Kalli Bidiyo: Sheikh Musa Asadussunnah yace kamar yanda ake shirin Titsiye, Malam Lawal Triumph a hada da Malam Nazifi Alkarmawi saboda yace idan mutum yayi mafarki ya ga Raqumi, Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya gani

Duk Labarai
Malam Musa Asadussunnah ya bayyana cewa, idan dai za'a Titsiye malam Lawal Triumph kan kalaman da yayi, to ya kamata a Hada da malam Nazifi Alkarmawi. Malam Musa yace, Shima Alkarmawi yace idan aka yi mafarkin Raqumi to kamar an ga Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ne. Yace amma babu wanda yaji yana sukar Alkarmawi aka wannan kalamai. Yace dan haka indai za'a titsiye malam Lawal Triumph to a hada da Alkarmawi. https://www.tiktok.com/@buharimandemgy/video/7555596889450630418?_t=ZS-909Y9F2iVEH&_r=1 https://www.tiktok.com/@muhammadsunnahaljosawy/video/7555545750835350802?_t=ZS-909bl2Injmb&_r=1
Babu ruwan mu da ta Halal ko ta Haram ka samu kudin shiga, Kowa, hadda Kharuwaiy sai sun fara biyan Haraji nan da shekarar 2026>>Inji Gwamnatin Tarayya

Babu ruwan mu da ta Halal ko ta Haram ka samu kudin shiga, Kowa, hadda Kharuwaiy sai sun fara biyan Haraji nan da shekarar 2026>>Inji Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa sabuwar dokar Haraji da zata fara aiki a shekarar 2026 ba ruwanta da anda mutum ya samu kudi, ko ta hanyar data kamata mutum ya samu ko bata hanyar dta kamata ba, dole ya biya Haraji. Shugaban Kwamitin shugaban kasa kan tsare-tsaren kudi da Gyara, Taiwo Oyedele ne a bayyana haka a cocin RCCG a wata ziyara da ya kai. Yace idan dai mutum zai sayar da wani abu ko zai aikata wani abu ya samu kudi, ba ruwan gwamnati da wane irin aiki ne mutum ya aikata, sai ya biya Haraji, kamar yanda kafar Peoplesgazette ta ruwaito. Gwamnatin tarayya dai na kokarin ganin ta karbi haraji daga kowane fanni na samun kudi dan ta tayar da komadar tattalin arzikin Najeriya.
Kalli Bidiyo: Saurayinta ya siyo mata wayar iPhone XR amma tace bata so sai dai ya siyo mata iPhone 13

Kalli Bidiyo: Saurayinta ya siyo mata wayar iPhone XR amma tace bata so sai dai ya siyo mata iPhone 13

Duk Labarai
Wannan wata matashiyace da ta jawo cece-kuce bayan da saurayinta a sai mata wayar iPhone XR amma tace bata so sai 13. A Bidiyon da ya watsu sosai, an ji yana cewa ta ce masa bata son iPhone X, shine ya kawo mata XR amma itama tace bata so ya kaiwa mabukata. Da yawa dai sun yi mamakin rashin godiyar Allah na Budurwar. Kalli Bidiyon anan
Dan Najeriya da aka turawa Dala dubu 135 cikin wallet dinsa ta Kyriptho, watau Kwatankwacin Naira Miliyan 200 bisa kuskure ya mayar wa da me kudin kayansa

Dan Najeriya da aka turawa Dala dubu 135 cikin wallet dinsa ta Kyriptho, watau Kwatankwacin Naira Miliyan 200 bisa kuskure ya mayar wa da me kudin kayansa

Duk Labarai
Dan Najeriya, Sunusi Danjuma Ali da aka turawa Dala dubu 135 a wallet dinsa na Crypto watau kwatankwacin Naira Miliyan 200 bisa kuskure ya mayarwa da me kudin kudinsa. An tura masa kudinne a Wallet dinsa ta Bitunix inda yana ganin hakan ya tuntubi wakilan kamfanin kuma suka tabbatar kuskurene aka yi wajan tura masa kudin. Nan da nan aka warware.
Kawuna a Legas yake zaune amma baya cin kifin da ake sayarwa a Legas, Kullun Idan zai ci kifi, Landan yake aikawa a siyo mai a doro a jirgin sama a kawo mai>>Inji Dan Forex, Dapo Wills

Kawuna a Legas yake zaune amma baya cin kifin da ake sayarwa a Legas, Kullun Idan zai ci kifi, Landan yake aikawa a siyo mai a doro a jirgin sama a kawo mai>>Inji Dan Forex, Dapo Wills

Duk Labarai
Shahararren dan Forex, Dapo Wills ya bayyana cewa, Kawunsa na zaunene a Legas amma idan zai ci Kifi, baya cin wanda ake sayarwa a Legas. Yace Landan yake aikawa a siyo kifin a sako mai shi a jirgi sannan a kawo ya ci. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi wadda ta watsu sosai a kafafen sadarwa. Kalli Bidiyon hirar a kasa: https://twitter.com/Teeniiola/status/1972242656970649655?t=ZnQXjyJyQe7-vNRxx9miVg&s=19