Friday, February 20
Shadow
Ji yanda wani ya Hàllàqà mahaifiyarsa saboda ya gaji da yi mata Hidima kuma ta tsufa sosai

Ji yanda wani ya Hàllàqà mahaifiyarsa saboda ya gaji da yi mata Hidima kuma ta tsufa sosai

Duk Labarai
Hukumomi a birnin Tokyo na kasar Japan sun kama wani mutum me suna Masato Watabe dan kimanin shekaru 79 bayan da ya hallaka mahaifiyarsa. Mahaifiyar tasa nada shekaru 100 a Duniya kuma shine ke kula da ita. Hukumomin birnin sun ce ya hallakata ne ya hanyar rufe mata baki. Mutumin dai da kansa ya kirawo 'yansanda. Kasar Japan na fama da karancin matasa inda manyan mutane masu yawan shekaru dole sune ke kula da iyayensu da shakeru suka kamasu.
Wannan wane irin rashin Tausai ne haka, Kalli Bidiyon Me gida ya watsar da kayan wani mutum da aka yi Ghàrkùwà dashi bayan kudin haya sun kare

Wannan wane irin rashin Tausai ne haka, Kalli Bidiyon Me gida ya watsar da kayan wani mutum da aka yi Ghàrkùwà dashi bayan kudin haya sun kare

Duk Labarai
Wannan Bidiyon ya dauki hankula a kafafen sadarwa inda ya nuna yanda wani me gidan haya ya watsawa wani mutuk kaya waje bayan da kudin hayarsa suka kare. Saidai abinda ya fi baiwa mutane mamaki shine mutumin na can a hannin Tshàgyèràn Dhàjì ana faman yanda za'a karboshi. Kuma me gidan ya sani amma yace ba ruwansa. https://twitter.com/General_Somto/status/1996932969584300229?t=0pcRTvihw2CAQImSneLNBA&s=19
Kalli Bidiyon yanda jami’in tsaron Civil Defence ke tonawa wani na hannun daman Gwamna Asiri cewa shine ke daukar nauyin Tshàgyèràn dake hana mutane zàmàn Lafiya

Kalli Bidiyon yanda jami’in tsaron Civil Defence ke tonawa wani na hannun daman Gwamna Asiri cewa shine ke daukar nauyin Tshàgyèràn dake hana mutane zàmàn Lafiya

Duk Labarai
Wannan wani jami'in Hukumar Civil Defence ne a jihar Imo da ya bayyana wani me suna, Chinasa Nwaneri da cewa shine ke daukar nauyin Tshàgyèràn dake aikata ayyukan Ashsha na hare-hare a jihar. Chinasa Nwaneri daya ne daga cikin masu taimakawa gwamnan jihar Imo na musamman akan ayyukansa. Wannan zargi dai yayi nauyi inda mutane ke cewa ya kamata a bincikeshi. https://twitter.com/General_Somto/status/1996841460642308532?t=d9ydlNYqHeWR7BwvdL3Ujg&s=19
Allah Sarki, Kalli Bidiyon yanda wani dan Najeriya ya sayi Buhun shinkafa ya rabawa mutane kyauta saboda murnar shugaba Tinubu ya nada janar Christopher Musa Ministan tsaro

Allah Sarki, Kalli Bidiyon yanda wani dan Najeriya ya sayi Buhun shinkafa ya rabawa mutane kyauta saboda murnar shugaba Tinubu ya nada janar Christopher Musa Ministan tsaro

Duk Labarai
Wannan wani matashi dan Najeriya ne da yace yana tsaka ds tafiya zuwa wani gari amma da yaji labarin an baiwa Janar Christopher Musa mukamin Ministan tsaro. Shine ya tsaya a wani kauye ya sayi Buhun shinkafa ya rabawa mutane kyauta. Yayi fatan cewa Allah ya baiwa sabon Ministan nasara ya kawo karshen matsalar tsaron Najeriya. https://twitter.com/ZagazOlaMakama/status/1996917787412025722?t=PFhCXZrlhsAi_5EPBBrEGA&s=19
Wata Sabuwa: Tshàgyèràn Dhàjì na jihar Borno sun bude gidan Rediyo suna yada shirye-shiryensu da yarukan Hausa, Kanuri, da Turanci

Wata Sabuwa: Tshàgyèràn Dhàjì na jihar Borno sun bude gidan Rediyo suna yada shirye-shiryensu da yarukan Hausa, Kanuri, da Turanci

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Borno na cewa kungiyar dake ikirarin Jihadi ta ÌŚWÀP ta fadada ayyukan gidan rediyonta inda take yada shirye-shiryenta da yarukan Hausa, Kanuri, da Turanci. Saidaj ba kaitsaye gidan Rediyon ke aiki ba, suna dauka ne sai a rika turawa kamar yanda ake tura waka ko fim, kamar yanda masanin harkar tsaro, BrantPhilip ya ruwaito. Ya kuma wallafa Sautin muryar daya daga cikin shirye-shiryen kungiyar da aka nada wanda aka yadashi da Turanci. https://twitter.com/BrantPhilip_/status/1996857715600007465?t=XK7ddJaXBlEmU-7-7FOPsg&s=19 Wannan lamari dai ya zowa mutane da mamaki inda da yawa suka rika tunanin yaushe Kungiyar har ta samu nutsuwar yin abubuwa haka?
Kalli karin Bidiyon giwayen da suka bayyana a jihar Borno

Kalli karin Bidiyon giwayen da suka bayyana a jihar Borno

Duk Labarai
A jiyane dai muka samu Rahoton cewa, Giwaye sun bayyana garin Kala Balge na jihar Borno inda mutane suka taru suna kallonsu. Zagazola Makama yace giwayen sun rika cinye amfanin gona inda yayi kira ga mahukunta dasu kaiwa jama'a dauki. Bidiyon da hotunan giwayen sun ci gaba da yaduwa a kafafen sada zumunta Wasu rahotanni sun ce giwayen sun shiga garin ne daga kasar Chadi. https://www.tiktok.com/@umarfaruq6966/video/7579953257259339029?_t=ZS-91y7VEZ0NGa&_r=1
Ji Abinda ya faru da shafukan sada zumunta na Hadiza Gabon bayan da Masoya Adam A. Zango suka sha Alwashin yin Unfollow dinta

Ji Abinda ya faru da shafukan sada zumunta na Hadiza Gabon bayan da Masoya Adam A. Zango suka sha Alwashin yin Unfollow dinta

Duk Labarai
Bayan da Hadiza Gabon ta ki saka hoton Adam A. Zango a dakin da take hira da mutane wanda ya jawo cece-kuce sosai. Daya daga cikin matakan da masoya Adam A. Zango suka sha alwashin dauka shine zasu yi Unfollow dinta a shafukan sada zumunta dan nuna bacin Ransu. Tun bayan shan wannan Alwashi yanzu sama da awanni 24 kenan Hutudole yana saka ido akan shafukan na sada zumuntar Hadiza Gabon dan ganin ko zata samu raguwar mabiya. Mutane musamman a kasashen Turawa sukan dauki irin wannan mataki na Unfollow ga wani da yayi wani abinda basa so. Saidai Hutudole har zuwa yanzu ya lura cewa Hadiza Gabon bata rasa mabiya ba ko kuma mabiyanta basu ragu ba a shafukanta na sada zumunta.
‘Yan majalisar jihar Rivers 16 sun bar PDP zuwa APC

‘Yan majalisar jihar Rivers 16 sun bar PDP zuwa APC

Duk Labarai
Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Rivers, Martin Amaewhule, ya sauya sheƙa tare da wasu ƙarin mambobi 15 na majalisar a ranar Juma’a, lamarin da ya ƙara dagula harkokin siyasar jihar wadda ke fama da rikice-rikicen cikin gida tun watanni da dama. Rahotanni sun nuna cewa sauya sheƙar na da alaƙa da rikicin siyasa da ya dabaibaye jihar. Wannan mataki ya mayar da adadin mambobin majalisar da suka koma jam’iyyar APC zuwa 16 gaba ɗaya. Sauya sheƙar ya faru ne a wani zama na musamman da majalisar ta yi inda mambobin suka bayyana cewa sun yanke shawarar komawa APC